'Rashin Darajar Naira Ka Iya Zama Alheri ', CBN Ya Fadi Yadda Za a Inganta Najeriya

'Rashin Darajar Naira Ka Iya Zama Alheri ', CBN Ya Fadi Yadda Za a Inganta Najeriya

  • Duk da karyewar darajar Naira a Najeriya, Babban Banki watau CBN ya bayyana yadda hakan zai iya zama alheri
  • Gwamnan babban bankin, Olayemi Cardoso ya ce duk da rashin darajar Naira akwai damarmaki da dama kan haka
  • Cardoso ya fadi haka yayin da Naira ke cigaba da samun nasaku idan aka kwatanta da farashin dala a kasuwanni

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi magana kan rashin darajar Naira a faɗin kasar.

Gwamnan babban bankin, Olayemi Cardoso ya fayyace amfanin Naira duk da rashin darajar da take da shi.

CBN ya fadi yadda za a yi amfani da rashin darajar Naira wurin kawo cigaba
Babban Bankin Najeriya, CBN ya ce akwai damarmaki a rashin darajar Naira. Hoto: Central Bank of Nigeriya, CBN.
Asali: Getty Images

Naira: Bankin CBN ya ba yan Najeriya shawara

Kara karanta wannan

"Allah ji ƙansu," Gwamnan Abba ya yi maganar mutuwar sama da mutum 100 a Jigawa

Daily Trust ta ce Cardoso ya bayyana haka ne a jiya Laraba 16 ga watan Oktoban 2024 yayin wani taro a Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan CBN ya ce rashin darajar Naira zai ba Najeriya damar bunƙasa fitar da kayanta zuwa ketare.

Bankin CBN ya ce akwai damarmaki da mutane za su yi amfani da su duk da rashin darajar kuɗin a kasuwa.

CBN ya ce akwai damarmaki duk faduwar Naira

"Abin da ya kamata mu yi a yanzu shi ne tabbatar da kasancewar masu zuba hannun jari a nan saboda rashin hakan barazana ne."
"Amma kuma hakan wata dama ce da zamu bunkasa harkokin fitar da kaya ketare."
"Hakan zai kara tabbatar da Najeriya cikin gasa da sauran ƙasashe kan kasuwanci da fitar da kayayyakinta."

- Olayemi Cardoso

Cardoso ya ce yana amfani da damar domin karawa mutane karfin guiwar cewa akwai damarmaki duk da matsalar farashin Naira, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

An fayyace wanda ke rike da Najeriya bayan ficewar Tinubu da Kashim daga kasar

Naira ta sake faduwa a kasuwar duniya

Kun ji cewa Naira ba ta ji da daɗi ba a hannun Dalar Amurka a kasuwar ƴan canji a ranar Juma'a, 27 ga watan Satumban 2024.

Darajar Naira ta koma N1,700/$ wanda wannan ita ce faɗuwa mafi muni da ta yi tun daga watan Fabrairun 2024 da muka ciki.

Sai dai a farashin gwamnati, darajar Naira ta ƙaru da kaso 2.24% daga kan farashin da aka sayar da ita a ranar Alhamis 16 ga watan Oktoban 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.