"Allah Ya Jiƙansu," Gwamnan Abba Kabir Ya Yi Magana kan Mutuwar Sama da Mutum 100

"Allah Ya Jiƙansu," Gwamnan Abba Kabir Ya Yi Magana kan Mutuwar Sama da Mutum 100

  • Gwamnan Kano ya yi ta'aziyyar mutanen da suka rasu sakamakon gobarar da ta tashi daga fashewar tankar mai a jihar Jigawa
  • Abba Kabir Yusuf ya bayyana rashin da aka yi a matsayin wanda ya shafi ƙasa baki ɗaya, inda ya yi addu'ar Allah ya jiƙan wadanda suka mutu
  • Mutane sama da 100 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu akalla 70 suka jikkata sakamakon fashewar tanka a garin Majiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya mika saƙon ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jigawa bisa ibtila'in fashewar tankar mai wanda ya yi ajalin mutane sama da 100.

Gwamna Abba ya bayyana lamarin wanda ya laƙume rayukan mutane sama da 100 tare da jikkata wasu da dama a matsayin babban abin takaici da ya shafi ƙasa baki ɗaya.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta kadu da faduwar tankar fetur a Jigawa, an fadi matakin da za a dauka

Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Gwamna Abba ya miƙa sakon ta'aziyya ga gwamnatin Jigawa bisa fashewar tanka da ya lakume rayuka Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Hakan dai na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda tanka ta fashe a Jigawa

Idan baku manta ba mun kawo maku rahoton yadda wata tanka maƙare da Fetur ta fashe a garin Majiya da ke ƙaramar hukumar Taura a jihar Jigawa.

Fashewar tankar ya tada mummunar gobara wadda ta zama ajalin mutane kusan 150 kawo yanzu, wasu akalla 70 na kwance ana masu magani a asibiti.

Da yake miƙa sakon ta'aziyya ga waɗanda lamarin ya shafa, Gwamna Abba ya yi Addu'ar Allah ya jiƙan waɗanda suka rasu kuma ya ba waɗanda suka ji rauni lafiya.

Gwamnatin Kano ta miƙa sakon ta'aziyya

"Mun samu labarin wata mummunar gobara da ta afku a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a Jigawa, wanda ya yi sanadin asarar rayuka tare da kwantar da wasu da dama a asibiti.

Kara karanta wannan

Sukar Tinubu: Kalaman sanatan APC na neman kara sanya shi cikin matsala

“A madadin gwamnati da jama’ar Kano, ina mika sakon ta’aziyya ga Gwamna Umar Namadi, gwamnati da al'ummar Jigawa, musamman iyalan wadanda suka rasu da mutanen garin Majiya."

- Abba Kabir Yusuf.

Gwamnati za ta binciki fashewar tanka a Jigawa

A wani labarin kuma gwamnatin tarayya ta nuna damuwa kan mummunan hadarin motar mai da ya laƙume rayuka da dama a jihar Jigawa.

Ministan fetur ya bayyana cewa ba za a bar abin ya tafi a banza ba, za a binciko sababin faruwar mummunan haɗarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262