Gwamnati Ta Kadu da Faduwar Tankar Fetur a Jigawa, An Fadi Matakin da Za a Dauka

Gwamnati Ta Kadu da Faduwar Tankar Fetur a Jigawa, An Fadi Matakin da Za a Dauka

  • Gwamnatin tarayya ta bayyana kaduwarta bisa asarar rayuka sama da 100 a gobarar tankar fetur da ya afku a jihar Jigawa
  • Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya mika ta’aziyya ga gwamnati da jama’ar jihar, inda ya ce gwamnati za ta taimaka
  • Mutane akalla 107 ne su ka riga mu gidan gaskia, yayin da wasu adadinsu ke kwance a asibitin su na samun kulawar likitoci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Jigawa – Gwamnatin tarayya ta shiga alhinin asarar rayuka bayan fashewar tankar fetur da ta salwantar da rayuka akalla 107 a Jigawa.

A daren Talata ne wata mota makare da man fetur ta kife a Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa, daga bisani jama’a su ka zo diba.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu za ta yi bincike kan mutuwar mutane sama da 100 a Jigawa

Tinubu
Gwamnatin tarayya ta jimamin rasuwar jama'a a gobarar tankar Jigawa Hoto: Kashim Shettima
Asali: Facebook

A sakon da hadimin ofishin mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Laraba, ya ce gwamnati ba ta ji dadin asarar rayuka da aka samu ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnati za ta tallafawa mutanen Jigawa

NTA News ta wallafa cewa gwamnatin tarayya ta yi alkawarin tallafawa mutanen da gobarar tankar fetur ta shafa ta dukkanin hanyoyin da su ka dace.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ya bayyana haka a madadin shugaba Bola Tinubu, tare da mika ta’aziyya ga gwamntin jihar Jigawa ga iyalan wadanda iftila’in ya shafa.

Gwamnati za ta duba matakan safarar fetur

Gwamnatin Bola Tinubu ta bukaci a fara duba kan dukkanin matakan da ake bi wajen safarar man fetur domin kare makamancin mummunan hadarin tankar Jigawa.

Mataimakin shugaban kasar nan, Kashim Shettima ya ce asarar rayuka da hadarin ya jawo babban iftila’i ne, tare da addu’ar Allah Ya sada mamatan da rahamarsa.

Kara karanta wannan

Bayan rasa rayuka a Jigawa, barci ya dauke direba, wata tankar fetur ta kama da wuta

Tankar fetur ta fadi a Jigawa

A wani labarin kun ji cewa wata tankar fetur ta fadi a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa, inda ta jawo asarar rayuka sama da 107, yayin da wasu ke kwance a asibitin.

Rundunar yan sandan Jigawa ta bayyana cewa sai da ta yi kokarin jama’a zuwa wurin da tankar ta fadi, amma ajali ya riga ya kira mutane da dama, kuma tuni aka birne su da ranar yau Talata.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.