An Kai wa Fulani Makiyaya Hari a Filato, Rayuka Sun Salwanta

An Kai wa Fulani Makiyaya Hari a Filato, Rayuka Sun Salwanta

  • Kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta yi tir da kisan wasu Fulani makiyaya a lokacin da su ke tsaka da kiwon dabbobinsu
  • Da ya ke bayyana sunayen wadanda aka kashe, shugaban kungiyar Babayo Yusuf ya ce har shanu masu tarin yawa aka harba
  • Ya ce sun sanar da hukumomin tsaro domin su bi wa Fulanin da aka kashe ba tare da sun aikata laifin komai ba hakkinsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Plateau- Kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta bayyana yadda wasu miyagun mutane su ka kai wa Fulani makiyaya farmaki a Filato.

Shugaban kungiyar, Babayo Yusuf ne ya tabbatar da hare-haren, inda ya ce an kashe wasu Fulani a lokacin da su ke kiwo.

Kara karanta wannan

'A fita zanga zanga,' Yadda aka yi rubdugu ga Tinubu kan tashin kudin fetur

Lewis
An kashe makiyaya biyu a Filato Hoto: Michael S. Lewis
Asali: Getty Images

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa an kashe makiyayan a kananan hukumomi daban-daban, sannan an sace wani bafulatanin da ke kiwon dabbobinsa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wadanne makiyaya aka kashe?

Shugaban kungiyar Miyetti Allah a Filato, Babayo Yusuf ya ce wasu miyagun mutane sun kashe Bashiru Iliyasu a kauyen Jol, karamar hukumar Riyom.

Sai kuma mutum na biyu da aka kashe mai suna Yahuza Idris a titin Maikatako da ke karamar hukumar Bokkos.

An fada wa jami'an tsaro kisan makiyaya

Kungiyar Fulani ta Miyetti Allah ta ce an harbe shanu da yawa a lokacin da wasu bata gari su ka kai harin ta'addancin kan Fulani makiyaya a Filato.

Kungiyar ta ce tuni ta sanar da jami'an tsaron farin kaya na (DSS) da yan sanda da sauran wadanda su ka dace domin a dauki matakin kwato hakkin mutanen.

Kara karanta wannan

'Ka biya mu daga tushe', Sarakuna a Arewa sun roki Tinubu kan biyansu hakkokinsu

Gwamna ya goyi bayan Fulani makiyaya

A baya mun ruwaito cewa gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda ya gargadi manoma kan noma wasu filaye da sauran labi a kananan hukumomi da Fulani ke kiwo a kai.

A cewar Sakataren gwamnatin jihar Katsina, Abdullahi Garba Faskari, an zauna tare da cimma matsaya tsakanin manoma da makiyaya kan daina noma a labin da ake kiwo.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.