Damagum: Kotu Ta Dakile Kwamitin Gudanarwar PDP, Ta ba da Sabon Umarni

Damagum: Kotu Ta Dakile Kwamitin Gudanarwar PDP, Ta ba da Sabon Umarni

  • Yayin da rikicin PDP ke kara ƙamari, kotu ta shiga lamarin inda ta dakatar da matakin kwamitin zartarwa
  • Babbar Kotun Tarayya da ke birnin Abuja ta haramta dakatar da Damagum daga mukaminsa na shugaban PDP
  • Wannan na zuwa ne bayan tsagin jam'iyyar PDP ta dakatar Umar Damagum a yau Juma'a 11 ga watan Oktoban 2024

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Babbar Kotun Tarayya ta yi hukunci bayan dakatar da shugaban PDP, Umar Damagum daga mukaminsa.

Kotun da haramtawa kwamitin zartarwa (NEC) da Majalisar Amintattu (BOT) dakatar da Damagum.

Kotu ta haramta dakatar da shugaban PDP
Kotu ta haramtawa kwamitin zartarwa dakatar da shugaban PDP, Umar Damagun. Hoto: Peoples Democratic Party, PDP.
Asali: Facebook

Kotu ta yi hukunci kan dakatar da Damagum

Alkalin kotun, Peter Lifu shi ya ba da wannan umarni a yau Juma'a 11 ga watan Oktoban 2024, cewar rahoton Channels TV.

Kara karanta wannan

Cikakken jerin gwamnonin CBN daga 1958 zuwa yau da manyan nasarorin da suka samu

Lifu ya ce Damagum ne zai cigaba da kasancewa a matsayin shugaban PDP har zuwa babban taronta a watan Disambar 2025.

Alkalin ya ba da wannan umarni ne bayan korafin da Sanata Umar El-Gash Maina ya shigar game da dakatar da Damagum.

Ya ce a sashe na 42 da 47 da kuma 67 na dokar PDP, za a iya zaben shugabannin jam'iyyar ne kawai lokacin babban taronta.

Damagum: Yadda aka dakatar da shugaban PDP

Wannan na zuwa ne bayan kwamitin gudanarwa karkashin jagorancin Umar Damagun ya dakatar da wasu jiga-jigan PDP.

Yayin zaman, an dakatar da sakataren yada labaran jam'iyyar, Debo Ologunagba da mai ba ta shawara kan shari'a, Kamaldeen Ajibade.

Jim kaɗan bayan daukar matakin, tsagin jam'iyyar ya dakatar shugabanta, Umar Damagun da sakatarenta, Sam Anyanwu.

Dan PDP ya yi tsokaci ga Legit Hausa

Wani magoyin bayan PDP a Gombe ya yi magana da Legit Hausa kan matakin da tsagin jam'iyyar ya dauka.

Kara karanta wannan

Reshe ya juye da mujiya: Shugaban APC ya shiga matsala bayan dakatar da Minista

Kwamred Abubakar Aliyu ya ce rikicin PDP zai yi matukar tasiri a babban taron jam'iyyar ta kuma zaben 2027 da ake tunkara.

Jigon PDP ya ce ya kamata masu ruwa da tsaki su kawo karshen matsalar bayan dakatar da Umar Damagum a muƙaminsa.

Ya ce duk da kotu da hana dakatarwar da aka yiwa Damagum, ya kamata a zauna domin dinke barakar da gaggawa.

Tsagin PDP ya nada sabon shugaban

Mun ba ku labarin cewa rikicin PDP ya sauya salo bayan nadin mukaddashin shugaban jam'iyyar ta kasa a yau Juma'a 11 ga watan Oktoban 2024.

Tsagin jam'iyyar PDP a Najeriya ya nada Ahmed Yayari Mohammed a matsayin mukaddashin shugabanta bayan dakatar da Umar Damagum.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.