Gwamna Zamfara Ya Yi Alhinin Kisan Jami'an Tsaro, Ya Ba da Tabbaci

Gwamna Zamfara Ya Yi Alhinin Kisan Jami'an Tsaro, Ya Ba da Tabbaci

  • Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa kan kisan da ƴan bindiga suka yi wa jami'an Askarawan Zamfara
  • Miyagun ƴan binɗigan sun hallaka jami'an tsaron ne a wani harin kwanton ɓauna da suka kai musu a ƙaramar hukumar Tsafe
  • Dauda wanda ya nuna alhininsa kan kisan ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta tallafawa iyalan jami'an tsaron da aka kashe

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Zamfara - Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya yi alhinin rasuwar jami’an tsaron rundunar Askarawan Zamfara da aka kashe a jihar.

Wasu miyagun bindiga ne suka kashe jami'an tsaron a wani harin kwantan ɓauna da suka kai a yankin Tsafe na jihar Zamfara.

Gwamna Dauda ya yi alhinin kisan jami'an tsaro a Zamfara
Gwamna Dauda Lawal ya yi ta'aziyya kan kisan jami'an tsaro Hoto: Dauda Lawal
Asali: Twitter

Gwamnan jihar Zamfara ya yi alhini

Kara karanta wannan

Kaico: Ana tsaka da cin amarci, ango ya kashe amaryarsa ta hanya mai ban tausayi

Gwamna Dauda Lawal ya nuna alhininsa ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Idris, ya fitar a ranar Talata a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Dauda ya bayyana kisan da ƴan bindigan suka yiwa jami'an tsaron a matsayin wani mummunan abu.

Ya yabawa jajircewar jami’an tsaron rundunar Askarawan Zamfara da sauran sojoji bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare rayukan jama’a.

Gwamna Dauda ya yi ta'aziyyar Askarawa

"Na samu rahoton wani mummunan harin kwantan ɓauna da ƴan bindiga suka kai jiya a ƙaramar hukumar Tsafe, inda suka kashe jajirtattun jami’an tsaro guda tara."
"Ina so na yi amfani da wannan damar na miƙa ta’aziyyata a madadin gwamnati da al’ummar jihar Zamfara ga iyalai da ƴan uwan jami'an tsaron."
"Ba za a taɓa mantawa da sadaukarwar da suka yi ba. Ina fatan waɗanda suka jikkata za su warke da wuri."

Kara karanta wannan

Daukar nauyin 'yan bindiga: Sanata ya yiwa Gwamnan PDP martani mai zafi

"Gwamnatina ta ƙudiri aniyar bayar da duk wani tallafi da ya dace ga iyalan jami'an tsaron da suka rasa rayukansu."

- Gwamna Dauda Lawal

Gwamna Dauda ya biya kuɗin giratuti

A wani labarin kuma, kun ji gwamna Dauda Lawal ya biya N9bn a matsayin kuɗin giratuti da ma'aikatan Zamfara ke bin bashi tun shekarar 2011.

Gwamna Dauda Lawal ya amince da fara biyan bashin kuɗin giratuti ne waɗanda ake bin jihar bashi a farkon watan Fabrairun 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng