Ba a Gama Koyon Taken Najeriya ba, Gwamnatin Tinubu Ta Kakabawa Ma’aikata

Ba a Gama Koyon Taken Najeriya ba, Gwamnatin Tinubu Ta Kakabawa Ma’aikata

  • Gwamnatin Tarayya ta dawo da sabon taken ma'aikatan Gwamnatin Tarayya domin kara musu kaimi da kishin kasa
  • Shugabar ma'aikatan Gwamnatin Tarayya, Didi Walson-Jack ta tabbatar da haka inda ta ce hakan yana da fa'ida
  • Wannan na zuwa ne bayan Gwmanatin Tarayya ta sauya taken Najeriya wanda har yanzu wasu ke cigaba da koyo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shugabar ma'aikatan Gwamnatin Tarayya, Didi Walson-Jack ta sake dawo da taken ma'aikatan Najeriya.

Walson-Jack ta ce an dawo da taken ne domin karawa ma'aikatan Gwamnatin Tarayya karsashi da kuma kishin aiki.

Gwamnatin Tinubu ta sake dawo da taken ma'aikata a Najeriya
Shugabar ma'aikatan Gwamnatin Tarayya ta sake dawo da taken ma'aikata a Najeriya. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

An dawo da taken ma'aikata a Najeriya

Punch ta ruwaito cewa Walson-Jack ta bayyana haka ne a yau Talata 8 ga watan Oktoban 2024.

Kara karanta wannan

Ma'aikatan NAFDAC sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani, sun bayyana dalili

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Walson-Jack ta ce hakan zai karawa ma'aikatan kaimi musamman wurin tabbatar da nasarar muradun Bola Tinubu.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an kirkiri taken ma'aikatan ne tun a shekarar 2018 domin kara musu kaimi, cewar rahoton ThisDay.

Muhimmancin taken ga ma'aikata a Najeriya

"Mun dawo da taken ma'aikata domin kara musu karsashi wanda za su rika yi da sauran yan Najeriya."
"Taken zai karawa ma'aikatan dagewa kan aikinsu da hana su cin hanci da samar da abin ake nema a aikin."
"Ina amfani da wannan dama domin godewa Bola Tinubu game da goyon baya da yake ba mu wurin kawo sauye-sauye."

- Didi Walson-Jack

Walson-Jack ta bukaci hadin kan ma'aikata wurin tabbatar da yin taken domin kara musu kwarin guiwa.

Gwamnatin Tinubu ta tsara biyan albashin N70,000

Mun ba ku labarin cewa Gwamnatin Tarayya ta fitar da jadawalin abin da kowane ma'aikaci zai samu a sabon mafi ƙarancin albashin da aka kawo.

Kara karanta wannan

Wike ya ba 'ya 'yan Buhari, manyan ƴan siyasa wa'adin mako 2 kan filayensu a Abuja

An kasafta tsarin yadda ma'aikatan gwamnati za mu samu albashi har na tsawon shekara bayan karin kudin da aka yi masu.

Hakan na zuwa bayan rahotanni sun tabbatar da fara biyan mafi ƙarancin albashin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.