N77,000: NYSC Ta Fadi Dalilin Kasa Fara Biyan Sabon Alawus

N77,000: NYSC Ta Fadi Dalilin Kasa Fara Biyan Sabon Alawus

  • Hukumar yi wa ƙasa hidima ta Najeriya (NYSC) ta bayyana dalilin kasa fara biyan sabon alawus ga masu yi wa ƙasa hidima
  • Shugaban hukumar NYSC, ya bayyana cewa ba a fara biyan N77,000 ba ne saboda har yanzu gwamnati ba ta saki kuɗaɗen ba
  • Birgediya Janar Yusha'u Ahmed ya bayyana cewa yana sa rai nan ba da jimawa za a fara biyan sabon ƙarin na alawus ga masu yi wa ƙasa hidima

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Shugaban hukumar yi wa ƙasa hidima ta Najeriya (NYSC), Birgediya Janar Yusha'u Ahmed, ya yi ƙarin haske kan dalilin rashin fara biyan sabon alawus ga masu yiwa ƙasa hidima.

Shugaban na NYSC ya bayyana cewa an samun jinkiri wajen fara biyan sabon alawus ɗin ne saboda har yanzu gwamnati ba ta sakarwa hukumar kuɗin yin ƙarin ba.

Kara karanta wannan

Ana cikin tsadar rayuwa Tinubu ya fadi lokacin da 'yan Najeriya za su gode masa

NYSC ba ta fara biyan N77,000 ba
NYSC ta ce gwamnati ba ta saki kudin sabon alawus ba Hoto: @Officialnyscng
Asali: Twitter

A cikin watan Satumba ne dai hukumar NYSC ta fitar da sanarwar yin ƙari a alawus ɗin masu yi wa ƙasa hidima daga Naira 33,000 zuwa 77,000.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa NYSC ba ta biya N77,000 ba?

A yayin wata hira da jaridar BBC Hausa, shugaban na NYSC, ya bayyana cewa duk da cewa an amince da yin ƙarin, har yanzu gwamnati ba ta saki kuɗi ba domin aiwatar da ƙarin na sabon alawus.

"Ba ma su yi wa ƙasa hidima kaɗai ba, har ma'aikatan hukumarmu an yi musu ƙarin kusan wata huɗu zuwa biyar, amma ba a fara biyansu ba, amma muna sa rai nan ba da jimawa ba, za a fara biya, amma har yanzu ba a sakar mana kuɗin ba."
''Bayanin da muka samu bai fayyace mana cewa yaushe za a fara biya ba, amma dai an tabbatar mana cewa an yi musu ƙari daga ranar 29 ga watan Yulin 2024."

Kara karanta wannan

Daukar nauyin 'yan bindiga: Sanata ya yiwa Gwamnan PDP martani mai zafi

- Birgediya Janar Yusha'u Ahmed

Shehu Sani ya buƙaci a yi wa mata ƙarin kuɗi

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya ce kamata ya yi gwamnatin tarayya ta ƙarawa mata ƴan NYSC alawus daga N33,000 zuwa N100,000.

Sanata Shehu Sani ya yabawa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu bisa ƙara alawi na matasa masu yi wa ƙasa hidima watau NYSC zuwa N77,000.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng