"Na Ji Zafi Sosai" Buhari Ya Magantu kan Iftila'in da Ya Faru a Niger, Ya Kora Ruwan Addu'o'i

"Na Ji Zafi Sosai" Buhari Ya Magantu kan Iftila'in da Ya Faru a Niger, Ya Kora Ruwan Addu'o'i

  • Yayin da ake cigaba da tsamo gawarwaki ta ayyukan ceto a jihar Niger, Muhammadu Buhari ya tura sakon ta'azziya
  • Buhari ya bayyana halin da ya shiga bayan samun labarin kifewar jirgin ruwa makare da mutane masu bikin Maulidi
  • Tsohon shugaban ya yi addu'ar Allah ya yi wa wadanda suka rasu rahama da fito da wadanda suka bace cikin koshin lafiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yi magana kan iftila'in da ya faru a jihar Niger.

Muhammadu Buhari ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa ransu yayin wani mummunan hatsarin jirgin ruwa.

Buhari ya jajanta bayan mutuwar mutane a hatsarin jirgin ruwa
Muhammadu Buhari ya yi ta'azziya game da kifewar jirgin ruwa a jihar Niger. Hoto: Muhammadu Buhari.
Asali: Facebook

Buhari ya kadu da hatsarin jirgin ruwa a Niger

Kara karanta wannan

Atiku ya yi ta'aziyyar yan maulidi 150 da ake fargabar sun mutu a hadarin jirgi

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Garba Shehu ya wallafa a shafin X a yau Juma'a 4 ga watan Oktoban 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin sanarwar, Buhari ya ce ya kadu da rashin da aka yi bayan kifewar jirgin ruwan da ke makare da masu zuwa bikin Maulidi.

Buhari ya ce ya ji zafin rashin da aka yi yayin da ake cigaba da tsamo gawarwaki da ceto wasu da lamarin ya rutsa da su.

Muhammadu Buhari ya yi ta'azziya ga jihar Niger

Ya tura sakon ta'azziya ga gwamnatin Niger da kuma al'ummar jihar kan wannan abin bakin ciki da ya afku.

"Ina alhini da jajantawa iyalan wadanda suka rasu a hatsarin jirgin ruwa."
"Ina addu'ar samun nasara wurin tsamo sauran wadanda suka makale."
"Muna addu'ar Allah ya jikan wadanda suka rasu da addu'ar Allah ya tseratar da wadanda suka bace cikin kishin lafiya."

Kara karanta wannan

“An samu tsaro a Najeriya”: Ribadu ya fadi bambancin gwamnatin Tinubu da Buhari

- Muhammadu Buhari

Tinubu ya kadu da hatsarin jirgin ruwa

Kun ji cewa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin a gudanar da bincike domin gano dalilin yawaitar haɗurran jiragen ruwa a Najeriya.

Shugaban ƙasar ya kuma jajantawa gwamnatin jihar Neja da da sauran al'umma bisa haɗarin jirgin da ya rutsa da kusan mutum 300.

Tinubu ya umarci hukumar NIWA ta lalubo hanyoyin da ya kamata a bi domin magance haɗurran kwale-kwale a sassan kasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.