Gwamna Zulum Ya Zagaya, Ya Gano Wadanda Suka Taimaka wajen Jawo Ambaliya

Gwamna Zulum Ya Zagaya, Ya Gano Wadanda Suka Taimaka wajen Jawo Ambaliya

  • Gwamna Babagana Umara Zulum ya ziyarci wasu wuraren da ambaliya ta yi gagarumar barna a jihar Borno
  • Mai girma Gwamnan ya yi takaicin yadda wasu su ka gina gidaje a gabar ruwa, wanda ke hana ruwa bin hanyarsa
  • Farfesa Zulum ya yi umarnin haramta gine-gine a bakin ruwa a Borno domin rage illar iftila'in ambaliya a nan gaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Borno - Gwamna Babagana Umara Zulum ya fusata da mutanen da su ka gina muhallansu a gabar ruwa a jihar Borno.

Gwamna Babagana Zulum ya dora alhakin karuwar matsalar ambaliya da aka samu a baya-bayan nan kan irin wadannan gidaje.

Kara karanta wannan

Murnar samun 'yanci: Gambo Sawaba da fitattun mata 2 da su ka jijiga siyasar Najeriya

Borno
Gwamnan Borno Babagana Zulum ya yi takaicin gina gidaje a hanyar ruwa Hoto: The Governor, Borno State Government
Asali: Facebook

A sakon da gwamnan ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya yi takaicin yadda gidajen bakin ruwa su ka tare hanyar da ruwan zai wuce.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce an samu gagarumar asara yayin ambaliyar, kuma irin wadannan gidaje ne su ka dagula lamarin ta hanyar hana ruwa gudu.

Gwamna ya yi takaicin ambaliya a Borno

Jaridar The Daily Trust ta wallafa cewa gwamna Babagana Zulum ya ziyarci wasu wuraren da ambaliya ya masu ta'adi sosai a ambaliyar da ta gabata.

Farfesa Zulum ya yi takaicin yadda ambaliya ta lalata hanyoyi, gadar saman Gwange, makarantu da wani asibitin haihuwa da ke Gwange.

Ambaliya: Gwamna ya hana gini a hanyar ruwa

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya haramta gina gidaje a gaba da kan hanyoyin ruwa a fadin jihar domin rage illar ambaliya.

Zulum ya ce za a kafa kwamiti da zai duba yadda aka yi gine-gine a hanyar ruwa da ba gwamnatin tarayya shawara kan lamarin.

Kara karanta wannan

1 Oktoba: Bayan lissafo matsaloli, gwamna ya fadi abin da ake bukata daga yan Najeriya

Gwamna Zulum ya raba kayan ambaliya

A baya mun ruwaito cewa gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya raba kayan tallafi ga mutanen da iftila'in ambaliya ya rutsa da su a Maiduguri.

Yayin kaddamar da tallafin, gwamna Babagana Zulum ya godewa gwamnatin tarayya da duk wadanda su ka tallafa da kudi da abinci domin taimakon jama'a.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.