Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Jam'iyyar APC, Sun Harbe Shi har Lahira a Jihar Arewa

Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Jam'iyyar APC, Sun Harbe Shi har Lahira a Jihar Arewa

  • Wasu ƴan bindiga sun kashe shugaban APC na ƙaramar hukumar Suru a jihar Kebbi, Alhaji Bako Bala a ranar Laraba
  • Hadimin gwamnan jihar, Zaidu Kofar Sabuwa, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce maharan sun rutsa jigon APC a gonarsa
  • Haka kan kuma an samu labari ƴan bindiga sun sace mutum ɗaya a yankin ƙaramar hukumar Bunza, sun harbi wani

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kebbi - Ƴan bindiga sun hallaka shugaban jam'iyyar APC na ƙaramar hukumar Suru a jihar Kebbi, Alhaji Bako Bala.

Bayanai sun nuna cewa ƴan ta'addan sun sace Alhaji Baƙo Bala ranar Laraba, 2 ga watan Oktoba, 2024, kana daga bisani suka kashe shi.

Taswirar jihar Kebbi.
Yan bindiga sun halaka jigon APC, Bako Bala a jihar Kebbi Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Mai ba gwamnan Kebbi shawara kan harkokin talabijin da rediyo, Alhaji Zaidu Bala Kofa Sabuwa shi ne ya sanar da hakan a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

Faɗa ya kaure, manyan ƴan bindigan Arewa da yaransu akalla 20 sun baƙunci lahira

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda miyagun suka kashe shugaban APC

Ya ce ƴan bindiga sun farmaki Baƙo Bala a gonarsa da ke mahaifarsa, kana suka harbe shi sannan suka tafi suka barshi cikin jini.

An garzaya da Alhaji Bako Bala zuwa asibitin FMC da ke Birnin Kebbi, inda aka yi rashin sa’a ya rasu a ranar Laraba sakamakon harbin da maharan suka yi masa.

...Ƴan bindiga sun harbi matashi a Kebbi

A wani lamari makamancin haka, wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wani mutum a kauyen Matseri da ke karkashin karamar hukumar Bunza a jihar Kebbi.

Rahotanni sun nuna maharan sun kuma harbi wani matashi a harin, wanda yanzu haka yana kwance a asibitin FMC ana masa magani.

Ba a iya jin bakin Ƴan sanda ba

Duk wani ƙokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kebbi, SP Nafiu Abubakar, kan kisan shugaban APC da harin sace mutumin ya ci tura.

Kara karanta wannan

Ma'aikatan jinya na shirin jefa mutanen Kano cikin matsala, sun ba gwamna wa'adi

Jihar Kebbi dai ta sha fama da sace-sacen mutane domin neman kudin fansa a 'yan kwanakin nan, duk da kokarin da jami'an tsaro ke yi na magance lamarin.

Ƴan sanda sun kama miyagu a Abuja

A wani labarin kuma rundunar yan sanda ta bayyana kama wasu hatsabiban yan ta'adda da su ka addabi Abuja da wasu jihohin Arewa.

Jami'ar hulda da jama'a ta rundunar ta reshen birnin Abuja, SP Josephine Adeh ta ce an kama mutane hudu a maboyarsu da ke birnin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262