Zanga Zanga Ta Barke a Sakatariyar Jam'iyyar PDP, an Samu Bayanai

Zanga Zanga Ta Barke a Sakatariyar Jam'iyyar PDP, an Samu Bayanai

  • An samu ɓarkewar wata zanga-zanga a sakatariyar jam'iyyar PDP ta Rivers da ke a birnin Port-Harcourt watau babban birnin jihar
  • Zanga-zangar ta ranar Alhamis, 3 ga watan Oktoban 2024 ta ɓarke ne domin nuna adawa da shirin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi
  • Masu zanga-zangar sun yi kira ga hukumar zaɓen jihar RSIEC da Gwamna Siminalayi Fubara su bi umarnin kotu kan zaɓen

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Rivers - Zanga-zanga ta ɓarke a sakatariyar jam’iyyar PDP da ke birnin Port-Harcourt babban birnin jihar Rivers.

Zanga-zangar da ta ɓarke a ranar Alhamis, 3 ga watan Oktoban 2024 ana yin ta ne kan zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

Zanga zanga ta barke a sakatariyar PDP da ke Rivers
Matasa sun fito zanga zanga a sakatariyar PDP da ke Rivers Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Tashar Channels tv ta rahoto cewa an jibge jami'an tsaro a sakatariyar jam'iyyar PDP da ke jihar.

Kara karanta wannan

Matasa sun barke da zanga zanga a ofishin INEC, sun fadi bukatunsu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa ake zanga-zanga a ofishin PDP?

Masu zanga-zangar dai sun yi dafifi a sakatariyar jam'iyyar PDP ne domin nuna adawarsu da shirin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin da ake yi a jihar.

Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, yawan masu zanga-zangar ya haifar da cunkoso a kan hanyar, yayin da jami’an tsaro ke ƙoƙarin shawo kan jama’a.

Daga baya an ga masu zanga-zangar ɗauke da alluna da tutoci, suna rera waƙoƙin nuna adawarsu da kuma yin guje-guje a kan babbar hanyar.

Ɗaya daga cikin tutocin na ɗauke da rubutu mai cewa:

"Mutanen TAI sun ce ba su son rashin bin doka. Ba mu son a yi zaɓen ƙananan hukumomi. Dole ne hukumar RSIEC ta bi umarnin kotu, dole ne Gwamna Simi ya bi umarnin kotu."

Gwamna Fubara ya ba da hutu

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ayyana ranakun Alhamis da Juma'a, 3 da 4 ga watan Oktoba, 2024 a matsayin ranakun hutu.

Kara karanta wannan

Ighodalo: Sabuwar zanga zanga ta ɓarke a hedkwatar hukumar INEC, bayanai sun fito

Gwamna Fubara ya ba da hutun kwanaki biyun ne domin bai wa ma'aikata damar komawa yankunansu domin kaɗa kuri'a a zaɓen kananan hukumomin da za a yi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng