'Yan Boko Haram Sun Yi Ta'addanci a Borno Ana Murnar Samun 'Yancin Kai

'Yan Boko Haram Sun Yi Ta'addanci a Borno Ana Murnar Samun 'Yancin Kai

  • Ƴan ta'addan Boko Haram sun yi garkuwa da wasu manoma a jihar Borno bayan sun kai musu farmaki a gona
  • Miyagun ƴan ta'addan sun yiwa biyar daga cikin manoman yankan rago bayan sun tafi da su zuwa sansaninsu
  • Harin wanda ƴan ta'addan Boko Haram suka kai a ƙaramar hukumar Gwoza ta jihar ya kuma yi sanadiyyar rasa ran wani jami'in tsaro na CJTF

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Borno - Ƴan ta'addan Boko Haram sun kashe aƙalla manoma biyar a wani mummunan hari a jihar Borno.

Ƴan ta'addan na Boko Haram sun kai harin ne a ƙauyen Ngoshe da ke ƙaramar hukumar Gwoza a jihar Borno.

'Yan Boko Haram sun kashe manoma a Borno
'Yan ta'addan Boko Haram sun yanka manoma a Borno Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Ƴan Boko Haram sun yi ta'asa a Borno

Kara karanta wannan

Sojoji sun samu gagarumar nasara kan 'yan ta'addan Boko Haram

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa majiyoyi sun bayyana cewa ƴan ta'addan sun yanka biyar daga manoman da suka sace.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƴan ta'addan sun farmaki manoman ne yayin da suke tsaka da gudanar da aiki a gona.

Ƴan ta'addan na Boko Haram sun kashe wani jami’in rundunar ƴan sa-kai ta CJTF, Jubril Zarana, wanda ya haɗa kai da jami’an tsaro wajen daƙile harin.

"Cikin alhini muke sanar da sace kimanin manoma 15 da suka haɗa da yara, mata, matasa da tsofaffi da ƴan ta’addan Boko Haram suka yi a Ngoshe, ƙaramar hukumar Gwoza."
"Bayan ƴan ta’addan sun kai mutanen zuwa sansaninsu sun yiwa mutane biyar yankan rago waɗanda suka haɗa da Isa Musa Moh’d Diyara, Doglas, Salawuddin Suleman Dauda Lawan, Maryam Gwambran, Matan Kaka Mobil Aga da Baba Amos."
"Daga baya ƴan ta’addan na Boko Haram sun sako mata uku daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da su."

Kara karanta wannan

Sojojin sama sun kai farmaki sansanin 'yan ta'adda, sun sheke miyagu masu yawa

- Wata majiya

Sojoji sun ceto mutane a hannun ƴan Boko Haram

A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun rundunar haɗin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) sun samu nasara kan ƴan ta'addan Boko Haram a Borno.

Dakarun sojojin sun samu nasarar ceto mutane 40 da ƴan ta'addan Boko Haram suka yi garkuwa da su a Borno da ke yankin Arewa maso Gabas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng