1 ga Oktoba: Abin da Ke Faruwa a Kano bayan Fara Zanga Zanga a Wasu Sassan Najeriya

1 ga Oktoba: Abin da Ke Faruwa a Kano bayan Fara Zanga Zanga a Wasu Sassan Najeriya

  • Mutanen Kano sun kauracewa zanga-zangar da ake yi ranar Talata 1 ga watan Oktoba a wasu sassan ƙasar nan
  • Rahotanni sun nuna wasu daga cikin mazauna jihar Kano sun yi zamansu a gida yayin da wasu kuma suka fita harkokinsu na yau da kullum
  • Amma wani matashi a Kano ya shaidawa Legit Hausa cewa akwai waɗanda suka fita sai dai ƴan sanda sun gano shirunsu, sun cafke su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Mazauna jihar Kano sun yi fatali da zanga-zangar da ake yi yau 1 ga watan Oktoba, 2024 kan tsadar rayuwa da yunwa a faɗin ƙasar nan.

Rahotanni sun nuna cewa mutanen Kano sun ƙauracewa fita kan tituna a wannan karon, sun ci gaba da harkokin kasuwancinsu na yau da kullum.

Kara karanta wannan

1 ga Oktoba: Kotu ta yanke hukunci kan zanga zangar da ake shirin yi, ta jero wurare 4

Taswirar Kano.
Galibin mutanen Kano ba su fita zanga-zangar 1 ga watan Oktoba ba Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Zanga-zanga: Abin da ke faruwa a Kano

Wakilin jaridar Daily Trust ya tattaro cewa sakamakon ayyana wannan rana a matsayin ranar hutu, da yawa mutanen Kano musamnan ma'aikata su zaɓi zama a gida.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan zanga-zanga da ake yi a wasu jihohi mai taken “FearlessInOctober" ta yaɗu ne a kafafen sada zumunta, watanni buyu bayan zanga-zangar da aka yi a Agusta.

Zanga-zangar guda biyu dai an shirya su ne duka domin nuna adawa da tsare-tsaren gwamnatin Tinubu, inda matasa suka nemi a dawo da tallafin mai.

Duk da abubuwan da suka faru na ɓarna da sace-sace a zanga-zangar watan Agusta, wannan karon Kanawa sun ce ba za a sake yaudararsu ba.

Kano: Mutane sun ci gaba da harkokinsu

An tataro cewa babu hayaniya a manyan tituna sannan babu cunkoson ababen hawa, yayin da masu shaguna da sauran kananan sana'o'i suka ci gaba da harkokinsu.

Kara karanta wannan

Rundunar ƴan sanda ta gargaɗi mutanen Kano kan zanga zangar da ake shirin yi

Binciken da aka yi a manyan kasuwanni kamar Kwari, Sabon Gari, Mawaka da Kurmi ya nuna cewa galibin ƴan kasuwa sun buɗe shaguna, ‘yan kalilan ne a rufe.

Legit Hausa ta tuntuɓi wani matashi a Kano, Sanusi Isiyaku, wanda ya shaida mana cewa babu wata zanga-zanga da ke wakana yau, mutane sun yi zamansu a gida.

Ƴan sanda sun kama wasu a Kano

Sanusi ya ce matasa sun yi zamansu a gida, wasu kuma sun buɗe wuraren kasuwancinsu, sai dai duk da haka wasu marasa ji sun fita zanga-zanga.

A cewarsa, ana zargin wasu mutane suka ɗauki nauyin matasan da suka fita, kuma nan da nan ƴan sanda suka cafke su bayan gano manufarsu.

"Muna zaune lafiya wannan karon, matasa sun yi zamansu a gida, na samu labarin akwai wasu ƴan ƙungiyoyi da suka fita to amma ƴan sanda suk cafke su bayan samun bayanan sirri," in ji shi.

Kara karanta wannan

1 ga Oktoba: Zanga zangar da ake shrin yi ta gamu da tangarɗa a Kaduna

Yan sanda tarwatsa mutane a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewa masu zanga-zanga a Abuja sun gamu da cikas yayin da 'yan sanda suka rika jefa masu barkonon tsohuwa

A ranar Talata, 1 ga watan Oktoba ne matasa suka fara gudanar da zanga zangar nuna adawa da tsadar fetur, kayan abinci da na masarufi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262