Tsohon Kwamishinan Ganduje Ya Gargadi Tinubu kan Manakisar Kwankwaso

Tsohon Kwamishinan Ganduje Ya Gargadi Tinubu kan Manakisar Kwankwaso

  • Tsohon kwamishina a mulkin Abdullahi Ganduje ya shawarci Shugaba Bola Tinubu kan alaka da Rabiu kwankwaso
  • Jigon APC, Musa Ilyasu Kwankwaso ya ce hadaka da tsohon gwamnan sai an yi taka tsan-tsan saboda zai iya cin amana
  • Hakan na zuwa ne bayan rade-radin cewa ana zama domin hadaka saboda ba Kwankwaso mukamin Minista a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Jigon APC a jihar Kano, Musa Ilyasu Kwankwaso ya gargadi Bola Tinubu kan halin Rabiu Kwankwaso.

Jigon APC na magana ne bayan rade-radin cewa Kwankwaso zai yi hadaka da APC domin samun mukamin Minista.

Jigon APC a Kano ya shawarci Tinubu kan alaka da Kwankwaso
Jigon APC ya shawarci Tinubu ya yi hankali kan hadaka da Rabiu Kwankwaso. Hoto: Musa Ilyasu Kwankwaso, Asiwaju Bola Tinubu, Rabiu Musa Kwankwaso.
Asali: Facebook

An gargadi Tinubu kan hadaka da Kwankwaso

Ilyasu Kwankwaso ya bayyana haka ne yayin zantawa da yan jaridu a Kano inda ya ce Kwankwaso ba abin yarda ba ne, cewar The Guardian.

Kara karanta wannan

Sanusi II ya magantu kan rigimar matatar Dangote da NNPCL, ya gano masu laifi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tsohon kwamishinan ya ce an samu bayanai cewa Kwankwaso na ganawa da Tinubu domin hadaka da APC.

Ya ce ya kamata Tinubu ya yi hankali da Kwankwaso saboda ba shi da tabbas musamman wurin rike amana.

Kwankwaso: Jigon APC ya ja kunnen Tinubu

"Akwai bayanai cewa Tinubu yana ganawa da Kwankwaso domin hadakar NNPP da APC, ya kamata a yi hankali kan haka."
"Ya kamata Tinubu ya hada da jiga-jigan APC a Kano cikin ganawar da suka hada da Sanata Barau da Ado Doguwa da Abdullahi Abbas har ma Abdullahi Ganduje."
"Dalilin fadan haka kuwa, na san wanene Kwankwaso, ba abu mai wahala ba ne ya ci amanar Bola Tinubu saboda haka kasancewar 'yan APC za su zama shaidu."

- Musa Ilyasu kwankwaso

Kwankwaso ya mgantu kan hadakar NNPP-PDP

Kun ji cewa tsohon kwamishina a jihar Kano, Musa Ilyasu Kwankwaso ya yi magana kan hadakar jiga-jigan jam'iyyun adawa game da zaben 2027.

Kara karanta wannan

Ana shirin korar Ministoci, Ministan Tinubu ya nada hadimi, ya gargadi yan kwangila

Kwankwaso ya ce Atiku Abubakar da Rabiu Kwankwaso da Peter Obi suna bata lokacinsu ne kan shirin kifar da Bola Tinubu ne.

Wannan na zuwa ne yayin da jiga-jigan jam'iyyun adawa suke shirin haɗaka ta musamman domin shirin zaben 2027 mai zuwa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.