Shugaba Tinubu Ya Damu da Matasa, Ya Shirya Yin Taron Kasa na Kwanaki 30

Shugaba Tinubu Ya Damu da Matasa, Ya Shirya Yin Taron Kasa na Kwanaki 30

  • Shugaban kasa Bola Tinubu ya ce za a gudanar da taron matasa na kwanaki 30 domin nemo mafita kan matsalolinsu
  • Ya ce za a dora alhakin zakulo matasan da za su halarci taron na kasa a wuyan wakilansu da ke gwamnati
  • Ana sa ran nusar da matasan muhimmmancin tafiyarsu a gwamnati da bayar da gudunmawa wajen cigaban kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa za a gudanar da gagarumin taron matasa na kasa inda za a tattauna da masu ruwa da tsaki.

A jawabinsa na ranar samun yanci a safiyar Talata, shugaban ya ce za a duba duk wasu matsaloli da kalubale da matasan kasar nan ke fuskanta.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: An gano illolin talauci, kungiya ta kawowa Tinubu shawara

Tinubu
Gwamnatin tarayya za ta gudanar da taron matasa na kwanaki 30 Hoto: Bayo Onanuga
Asali: Facebook

Jaridar Premium Times ta wallafa cewa shugaban ya ce za a shafe kwanaki 30 ana tattaunawa domim samarwa matasan Najeriya mafita.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya fadi dalilin taron matasa

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ce za a gudanar da taron matasa na kwanaki 30 domin karfafa masu gwiwa wajen tallafawa gina kasa.

Ya ce za a bullo da hanyar tabbatar da an rika sa matasa cikin harkokin gwamnati da fito da tsare-tsaren da za su inganta rayuwarsu.

Tinubu zai tattaro matasan Najeriya

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa za a tattaro matasa daga sassan kasar nan daban-daban domin a tattauna mafita kan matsalolinsu.

Ya ce za a zabo matasan da za su halarci taron na kwanaki 30 ta hanyar aiki tare da wakilansu a gwamnatin Najeriya.

Matasa sun yi mamakin taron kwana 30

Kara karanta wannan

Zanga Zanga: Kungiyoyin Arewa sun amsa kiran fitowa tituna a ranar 1 ga Oktoba

Shugaban gamayyar kungiyoyin fararen hula a Kano, Ambasada Ibrahim Waiya kuma shugaban kwamitin zaman lafiya na Kano ya ce sun yi mamakin tsayin kwankin da shugaban kasa ya ce za a yi taro.

Ya ce amma babu mamaki akwai manufar da ake so a cimma na cigaban matasa a taron da za a gudanar na nemawa jama'a mafita.

Matasa na adawa da manufofin Tinubu

A baya mun ruwaito cewa kungiyar 'Northern Youth Council of Nigeria' ta ayyana shirinta na gudanar da zanga-zangar kwana daya domin nuna adawa da yunwa a kasar nan.

Za a gudanar da zanga-zangar a ranar Talata, 1 Oktoba 2024 domin nunawa gwamnatin tarayya rashin jin dadi kan yadda aka yi biris da yan Najeriya cikin talauci da rashin tsaro.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.