‘Ka Yi Hankali,’ Dattawan Arewa Sun Gargadi Tinubu kan Korar Ministoci

‘Ka Yi Hankali,’ Dattawan Arewa Sun Gargadi Tinubu kan Korar Ministoci

  • Wata kungiya a Arewacin Najeriya ta yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan maganar sauya ministoci da zai yi
  • Kungiyar ta ce akwai ministocin da suka nuna zalaƙa a karkashin mulkin Bola Tinubu da bai kamata a sauya su ba kwata kwata
  • A makon da ya wuce ne gwamnatin tarayya ta sanar da shugaban kasa Tinubu zai yi sauye sauye a cikin majalisar zartarwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Wata kungiyar dattawan Arewa maso yammacin Najeriya ta yi kira ga shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Kungiyar ta ce ya kamata shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi taka tsan-tsan wajen yunkurin sauya wasu ministoci.

Kara karanta wannan

Oktoba: An fadawa Tinubu sirrin shawo kan matasa masu shirin zanga zanga

Bola Tinubu
An ba Tinubu shawara kan sauya ministoci. Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Asali: Twitter

Jaridar Punch ta ruwaito cewa shugaban kungiyar, Dakta Adamu Giwa ne ya yi kiran ga shugaba Bola Ahmed Tinubu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gargadi Tinubu kan korar ministoci 3

1. Ministan gidaje

Wata kungiyar dattawan Arewa maso Yammacin Najeriya ta ce ministan harkokin gidaje, Ahmad Dangiwa ya yi kokari sosai.

Kungiyar ta kafa dalilin cewa ministan ya kawo tsare-tsaren da suka kawo sauyi wajen samar da gidaje ga ma'aikata.

2. Ministan kasafin kudi

The Guardian ta wallafa cewa ƙungiyar ta ce ministan tsare-tsare da kasafin kudi, Abubakar Atiku Bagudu ya nuna zalaƙa sosai.

A cewar kungiyar, Atiku Bagudu ya nuna kwarewa wajen fito da tsare-tsaren da suka sanya gwamnati kashe kudi a kan ƙa'ida.

3. Ministan tsaro

Kungiyar ta ce karamin ministan tsaro, Bello Matawalle ya nuna bajinta wajen jawo kashe manyan jiga jigan yan bindiga a Arewa.

Kara karanta wannan

Garambawul: Tinubu zai sallami ministoci 11 da wani babban jami'in gwamati

Saboda haka shugaban kungiyar ya ce ya kamata shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi sakayya mai kyau ne ga ministocin ba wai korar su ba.

Tinubu ya ci bashin $1.57bn

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta kara kinkimo bashin $1.57bn daga bankin duniya domin ayyuka na musamman.

An ruwaito cewa Bankin Duniya ya amince da ba gwamnatin tarayya bashin ne domin yin ayyuka na musamman guda uku a fadin Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng