Yadda NNPCL Ya Gano Satar Mai Har Zuwa Masallatai da Coci, Ya Dauki Mataki

Yadda NNPCL Ya Gano Satar Mai Har Zuwa Masallatai da Coci, Ya Dauki Mataki

  • Kamfanin mai na NNPCL ya bayyana yawan asara da yake yi musamman saboda satar mai da ake yi a Najeriya
  • Kamfanin ya koka kan yadda ya bankado yawan sace-sacen tare da gano wasu bututun mai zuwa wuraren ibada
  • Jami'in yada labarai a kamfanin, Olufemi Soneye ya tabbatar da cewa an lalata matatun mai ba bisa ka'ida kusan 8,000

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kamfanin mai na NNPCL ya yi magana kan yawan satar man da ake yi yanzu a Najeriya.

Kamfanin ya nuna damuwa kan yadda ya gano sabon salo na satar mai din har wuraren ibada da masarautu.

NNPCL ta gano yadda ake satar mai har a masallatai da coci
Kamfanin NNPCL ta koka kan yawan satar mai da ake yi a Najeriya. Hoto: NNPC Limited.
Asali: Facebook

NNPCL ta koka kan yawan satar mai

Kara karanta wannan

Sanata ya cigaba da tonon silili, ya fallasa rashin gaskiyar ‘yan siyasar kasar nan

Jami'in sadarwa na kamfanin, Olufemi Soneye shi ya tabbatar da haka a jiya Asabar 28 ga watan Satumbar 2024, cewar The Guardian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Soneye ya ce tabbas a yanzu satar ta yi yawa wanda har wuraren ibada sun gano bututun mai da ake amfani da su.

Ya ce kamfanin ya samu nasarar kara samar da mai daga ganga miliyan 1.7 zuwa ganga miliyan uku inda ya ce babban cigaba ne.

Yawan matatun mai da aka lalata

Mataimakin manaja a sashen kula da harkokin kamfanin NNPCL, Murtala Mohammed a bangarensa ya bayyana yadda ake satar a bayyane.

Mohammed ya ce akalla matatatun mai 8,000 ne aka lalata wadanda aka samar da su da yawa ba bisa ka'ida ba.

Jami'in ya ce an lalata matatun ne da aka samar ba bisa ka'ida ba a cikin watanni shida kacal da suka gabata.

Kara karanta wannan

NAGGMDP: Likitoci za su tsunduma yajin aiki a jihar Kano, bayanai sun fito

Tinubu ya magantu kan rigimar Dangote, NNPCL

Kun ji cewa Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi magana kan rigimar da ke faruwa tsakanin kamfanin NNPCL da matatar Aliko Dangote.

Fadar shugaban kasa ta ce Tinubu ba zai tsoma baki kan rigimar da ke faruwa tsakaninsu ba saboda suna cin gashin kansu.

Wannan na zuwa ne yayin da aka fara takun-saka tsakanin kamfanonin guda biyu tun bayan Dangote ya fara fitar da mai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.