Rai Baƙon Duniya: Mahaifiyar Tsohon Gwamna a Arewa Ta Kwanta Dama

Rai Baƙon Duniya: Mahaifiyar Tsohon Gwamna a Arewa Ta Kwanta Dama

  • Tsohon gwamnan jihar Taraba, Rabaran Jolly Nyame ya tafka babban rashi bayan mutuwar mahaifiyarsa a jiya Asabar
  • Marigayiyar, Mama Jummai Eli Nyame Kala ta rasu ne cikin salama a daren jiya Asabar 28 ga watan Satumbar 2024
  • Sakataren yada labaran tsohon gwamnan, Hon. Obidah Bitrus shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da ya fitar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Taraba - Mahaifiyar tsohon gwamnan jihar Taraba, Rabaran Jolly Nyame ta riga mu gidan gaskiya.

Marigayiyar mai suna Jumai Eli Nyame ta rasu ne a daren jiya Asabar 28 ga watan Satumbar 2024.

Mahaifiyar tsohon gwamna ta riga mu gidan gaskiya
Mahaifiyar tsohon gwamnan Taraba, Jolly Nyame ta riga mu gidan gaskiya. Hoto: Rev. Jolly Nyame.
Asali: Getty Images

Mahaifiyar tsohon gwamnan Taraba, Nyame ta rasu

Leadership ta ruwaito cewa sakataren yada labaran tsohon gwamnan, Hon. Obidah Bitrus shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa.

Kara karanta wannan

Rigima ta barke da dattawa suka kalubalanci gwamna kan nadin sabon sarki

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bitrus ya ce dattijuwar ta rasu ne cikin salama da misalin karfe 10.00 na daren ranar Asabar 28 ga watan Satumbar 2024.

"Cikin alhini mu ke sanar da rasuwar uwa kuma kaka a gare mu mai suna Mama Jummai Eli Nyame Kala."
"Mama, ita ce mahaifiyar tsohon gwamnan jihar Taraba, Jolly Nyame da ya yi mulki jihar har wa'adi uku."
"Ta rasu a daren ranar Asabar 28 ga watan Satumbar 2024 da misalin karfe 10.00 cikin salama."

- Hon. Obidah Bitrus

Gudunmawar da marigayiyar ta bayar a rayuwarta

Bitrus ya bayyana irin gudunmawar da dattijuwar ta bayar wurin inganta rayuwar al'umma da dama yayin da take raye.

Ya ce tabbas za a yi rashin Mama kuma ba za a taba mantawa da ita saboda taba rayuwar mutane da ta yi.

Hukumar EFCC ta cafke tsohon gwamnan Taraba

Kara karanta wannan

Rigima ta yi kamari da Gwamna ya zargi mataimakinsa da shirin kutse a gidan gwamnati

A wani labarin, kun ji cewa hukumar EFCC ta kama tsohon gwamnan jihar Taraba da ke Arewacin Najeriya, Architect Darius Ishaku.

Hukumar yaki da cin hanci ta cafke Ishaku kan zargin badakalar makudan kudi har N27bn a ranar Juma'a 27 ga watan Satumbar 2024.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an kama tsohon gwamnan ne a gidansa da ke birnin Abuja a daren ranar Juma'a kan zargin laifuffuka 15.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.