1 ga Oktoba: Masu Shirya Sabuwar Zanga Zanga Sun Aika Saƙo ga Ƴan Sandan Najeriya

1 ga Oktoba: Masu Shirya Sabuwar Zanga Zanga Sun Aika Saƙo ga Ƴan Sandan Najeriya

  • Masu shirya zanga-zanga a faɗin Najeriya ranar 1 ga watan Oktoba sun buƙaci tsaro daga rundunar ƴan sanda domin komai ya tafi lafiya
  • Hakan na kunshe a wata sanarwar haɗin guiwa da ƙungiyoyin da ke shirya zanga-zangar suka fitar, sun koka kan halin tsadar rayuwa
  • Ƙungiyoyin sun koka kan yadda hauhawar farashi ke ƙaruwa sakamakon ƙarin farashin litar man fetur da aka yi kwanan nan a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Masu shirya zanga-zangar da za a yi ranar ƴancin kai watau 1 ga watan Oktoba, 2024 sun aika wasiƙa zuwa ga rundunar ƴan sandan Najeriya.

Masu shirya zanga-zangar kan tsadar rayuwa sun buƙaci rundunar ƴan sanda ta ba su kariya a lokacin da suka fito kan tituna domin nuna fushinsu kan halin da ake ciki.

Kara karanta wannan

Kungiyar NLC ta tsunduma yajin aiki, an samu bayanai

Masu zanga zanga.
Masu shirya zanga zanga a watan Oktoba sun bukaci ƴan sanda su samar masu da tsaro Hoto: NurPhoto
Asali: Getty Images

Hakan na kunshe ne a wata sanarwar haɗin guiwa da ƙungiyoyin ERC, MFC, YRC, JAF da PACOR suka fitar, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matasan sun koka kan tsadar fetur

Kungiyoyin sun koka kan tashin farashin man fetur daga N200 a shekaru biyu da suka wuce zuwa N900 ko sama da haka a wasu sassan ƙasar nan.

Sun ƙara da cewa yunwa ta fara neman kai mutane kasa saboda tsadar man fetur da hauhawar farashin kayayyaki musamman abinci, Punch ta ruwaito.

A cewar ƙungiyoyin, a yanzu sabon mafi ƙarancin albashi na N70,000 da aka amince da shi ba zai ragewa ma'aikatan gwamnati raɗaɗin komai ba.

Wannan dai na zuwa ne kusan watanni biyu bayan zanga-zangar da matasa suka yi a watan Agusta, wadda ta rikiɗa ta zama tashe-tashen hankula da sace-sace.

Yadda matasa suka shirya zanga-zanga

Kara karanta wannan

NYSC: Matasa ƴan bautar ƙasa za su warwasa, an ƙara masu alawus duk wata

Amma a wannan karon za a yi zanga-zangar ne a ranar da Najeriya ke cika shekara 64 da samun ƴancin kai daga turawan mulkin mallaka.

Hassan Soweto, jagoran kungiyar ERC ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar cikin lumana don nuna adawa da "manufofin da suka kawo talauci"

Ya ce za su fara zanga-zanga a Legas da karfe 7:30 na safiya kuma za su haɗu a ƙarƙashin gadar Ikeja, inda za su bi tituna domin wayar da kan jama'a.

Masu shirya zanga-zanga sun jero buƙatu 17

A wani rahoton kuma matasan Najeriya na cigaba da shirye shiryen gudanar da zanga zangar adawa da tsadar rayuwa karo na biyu.

A wannan karon, matasan sun fitar da wasu jerin bukatu 17 ɗa suke buƙatar gwamnatin tarayya ta cika musu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262