Sarki Sanusi II Ya Yiwa Jonathan Martani kan Tsige Shi daga Gwamnan CBN a 2013
- Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya ce ko kadan ba ya jin haushin tsohon shugaban kasa Godluck Jonathan kan abin da ya faru 2013
- Muhammadu Sanuisi II ya nuni da cewa bai dauki tsohon shugaban da gaba ba duk da ya tsige shi daga gwamnan babban bankin Najeriya
- Hakazalika, sarkin ya yi magana kan wadanda ke kawo cikas ga matatar man Dangote yayin da ta fara aikin tace danyen mai a Legas
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Mai martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya jaddada cewa babu wata kiyayya tsakaninsa da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.
Muhammadu Sanusi II ya ce ko kadan bai kullaci Jonathan kan tsige shi daga matsayin gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) a shekarar 2013 ba.
Sanusi II ya yiwa Jonathan martani
Bayanin Sanusi II na zuwa ne bayan Jonathan ya musanta zargin cewa dala biliyan 49.8 sun bace a lokacin da ya ke shugaban kasa, inji rahoton Guardian.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
"Na san cewa kowa na so na yi martani amma ba zan yi ba. Lokacin da aka ce in fito in yi jawabi, na fada Sir D. Kusman cewa ba zan yi magana kan lamarin ba.
"Ina matukar girmama shugabana. Amma zan ce wani abu kadan. Na farko dai, ina ci gaba da girmama shugabana, Jonathan kuma babu kiyayyarsa ko ta wani a raina."
- A cewar Sarki Sanusi.
Mai martaba ya yi nuni da cewa lokacin da aka tsige shi daga gwamnan CBN ya zama sarki, bayan an tube rawaninsa ne ya ya samu matakin karatun PhD inda kuma yanzu ya ke kan kujerar Sarkin Kano.
Sarki ya magantu kan matatar Dangote
Sarkin na Kano ya kuma ce wasu masu hannu da shuni, wadanda suke samun arziki daga shigo da mai cikin kasar na kawo cikas ga matatar Dangote.
"Me zai sa har wani ya dakatar da mu daga sarra fetur da kanmu? Ba zai wuce saboda akwai masu hannu da shuni da ke samun arziki daga ci gaba da shigo da man ba.
"Wacce hanya za mu bi mu ganar da Najeriya cewa ita kasa ce da ke wakiltar jama'a ba wai kasar da wasu tsirarun masu mulki juya akalarta ba.? Wannan darasi ne babba."
Asali: Legit.ng