Zanga Zangar Oktoba: 'Yan Sanda Sun Fadi Dalilin Gayyatar Shugaban Matasa

Zanga Zangar Oktoba: 'Yan Sanda Sun Fadi Dalilin Gayyatar Shugaban Matasa

  • Yayin da ake shirin gudanar da zanga-zanga a ranar 1 ga watan Oktoban 2024, yan sanda a Lagos sun gayyaci shugaban matasa
  • Kwamishinan yan sanda a jihar, Olanrewaju Ishola ya ce sun dauki matakin ne domin tattauna wasu batutuwa kan lamuran kasa
  • Yan sanda sun gayyaci shugaban kungiyar 'Take it Back Movement', Juwon Sanyaolu da ya jagoranci zanga-zanga a Agusta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Lagos - Rundunar yan sanda ta gayyaci shugaban masu shirya zanga-zanga a ranar 1 ga watan Oktoban 2024.

Rundunar ta gayyaci Juwon Sanyaolu wanda ke jagorantar kungiyar 'Take it Back Movement' da ta yi zanga-zanga a watan Agustan 2024.

Kara karanta wannan

UNGA79: Bayan Najeriya ta ranto N87.38trn, Tinubu ya nemi afuwa ga kasashen Afrika

Rundunar yan sanda ta nemo hanyar dakile gudanar da zanga zanga
Yan sanda sun kira shugaban kungiyar matasa kan shirin zanga-zanga. Hoto: Nigeria Police Force.
Asali: UGC

Zanga-zanga: Yan sanda sun kira shugaban matasa

Kwamishinan yan sanda, Olanrewaju Ishola shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da The Guardian ta samu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ishola ya ce sun gayyaci Sanyaolu ne da sauran mambobinsa domin tattaunawa kan lamura da dama da suka shafi Najeriya.

Za a gudanar da ganawar a yau Laraba 25 ga watan Satumbar 2024 a ofishin kwamishinan da ke Ikeja a Lagos.

Dalilin neman shugaban masu zanga-zanga

Kakakin rundunar yan sanda a jihar Lagos, Benjamin Hundeyin ya bayyana yadda ganawar za ta kasance.

Hundeyin ya ce ganawa ce ta musamman amma babu shirin cafke wani daga cikinsu, cewar rahoton Punch.

"Shirin gudanar da zanga-zangar ranar 1 ga watan Oktoban 2024 na daga cikin abin da za a tattauna."
"Ba fada ba ne ko kuma wani tashin hankali, ko da bai halarta ba, babu wani abu da zai faru."

Kara karanta wannan

Zanga zangar Oktoba: Matasa sun fitar da zafafan bukatu 17 ga Tinubu

- Benjamin Hundeyin

Zanga-zanga: Matasa sun lissafo bukatu ga Tinubu

Kun ji cewa matasan Najeriya na cigaba da shirye shiryen gudanar da zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a karo na biyu.

A wannan karon, matasan sun fitar da wasu jerin bukatu 17 domin Gwamnatin Tarayya ta cika musu domin hana zanga-zanga.

Wannan na zuwa ne bayan gudanar da zanga-zanga daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024 saboda halin rayuwa da aka shiga.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.