Zargin Almundahana: Kotu Ta Dage Shari'ar Yahaya Bello da Hukumar EFCC

Zargin Almundahana: Kotu Ta Dage Shari'ar Yahaya Bello da Hukumar EFCC

  • Babbar kotun tarayya, mai zamanta a Abuja, ta dage sauraron zargin almundahana da ake yi wa tsohon gwamna, Yahaya Bello
  • Hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ce ke zargin tsohon gwamnan da handame sama da N80bn daga asusun Kogi
  • Mai Shari'a Emeka Nwite ya dage sauraron shari'ar zuwa watan Oktoba, inda ake jiran hukuncin kotun koli kan karar da Bello ya shigar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

FCT, Abuja - Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage sauraren shari'ar tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello da za a yi a yau zuwa watan gobe.

Mai Shari'a Emeka Nwite ne ya bayyana hukuncin a ranar Laraba bayan tsohon gwamnan ya nufi kotun koli domin neman a soke umarnin kama shi da babbar kotu ta yi.

Kara karanta wannan

Murna za ta koma ciki: Kungiyar APC na shirin daukaka kara kan nasarar Ganduje

Yahaya Bello
Kotu ta dage sauraron shari'ar tsohon gwwamnan Kogi Hoto: Yahaya Bello/EFCC
Asali: Facebook

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC), na zargin Yahaya Bello da almundahana da halasta kudin haram.

Yahaya Bello ya nufi kotun koli

Jaridar Independent ta wallafa cewa lauyan Yahaya Bello, A.M Adoyi ya shaidawa kotu cewa zaman na yau Laraba ba zai yiwu ba saboda maganar na gaban kotu ta gaba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Barista A.M Adoyi ya kara da cewa abin da ya dace kotu ta yi shi ne dakatar da shari'ar har sai kotun koli ta yanke hukunci kan karar da Yahaya Bello ya shigar.

EFCC ta soki lauyan Yahaya Bello

Lauyan hukumar EFCC, Kemi Pinheiro SAN ya zargi lauyan Yahaya Bello da kokarin mayar da kotu wajen wasa da raha.

Ya kara da cewa ko a baya, kotun daukaka kara ta soke bukatar Yahaya Bello na kalubalantar hanyar da EFCC ke bi na gurfanar da shi gaban kotu.

Kara karanta wannan

Baki har kunne: Shugaban APC, Abdullahi Ganduje ya samu manyan nasarori a cikin mako 1

Mai Shari'a Emeka Nwite ya dage sauraron karar zuwa ranar 30 Oktoba, 2024.

Yahaya Bello na wasan buya da EFCC

A baya mun ruwaito cewa bayan an samu musayar kalamai tsakanin hukumar EFCC da tsohon gwamna Yahaya Bello, tsohon gwamnan ya tsere inda ake nemansa yanzu ruwa a jallo.

Duk da Yahaya Bello ya bayyana cewa ya mika kansa ga hukumar EFCC, amma hukumar ta musanta batun, inda ta bayyana cewa tsohon gwamnan ya yi batan dabo.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.