Mutuwar Sanata Ta Dakatar da Zaman Majalisar Tarayya, Bayanai Sun Fito

Mutuwar Sanata Ta Dakatar da Zaman Majalisar Tarayya, Bayanai Sun Fito

  • Majalisar wakilai ta ɗage zamanta na farko bayan dawowa daga hutun shekara-shekara domin jimami da karrama marigayi Sanata Ifeanyi Ubah
  • Sanatan mai wakiltar Anambra ta Kudu a majalksar dattawa ya riga mu gidan gaskiya ne a watan Yuli lokacin ƴan majalisa sun tafi hutu
  • Kamar yadda al'adar majalisar tarayya ta tanada, idan ɗan majalisa ya rasu, a kan ɗage zaman ranar farko, an sanar da sai Laraba za a dawo zama

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Majalisar wakilai ta tarayya ta ɗage zamanta na yau Talata, 24 ga watan Satumba, 2024 domin karrama marigayi Sanata Ifeanyi Uba.

A yau majalisar ta ke dawowa daga hutun shekara-shekara wanda kundin tsarin mulki ya tanada, to sai dai ta ɗage zamata zuwa gobe Laraba domin girmama marigayin.

Kara karanta wannan

Gwamna ya bi sahun Adamawa, ya faɗi watan da zai fara biyan sabon albashin N70,000

Marigayi Sanata Ifeanyi Ubah.
Majalisar wakilan tarayya ta ɗage zama domin karrama marigayi Sanata Ifeanyi Uba Hoto: Nigerian Senate
Asali: Facebook

Sanata Ubah ya rasu a Landan

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, Sanata Ubah mai wakiltar Anambra ta Kudu ya mutu ne ranar 27 ga watan Yuli, 2024 a lokacin majalisar ta tafi hutu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan matakin da majalisar wakilai ta dauka ya yi daidai da al’adar majalisar dokokin Najeriya na dakatar da zaman farko idan wani ɗan majalisa ya kwanta dama.

Bayanai sun nuna Sanata Ifeanyi Ubah ya riga mu gidan gaskiya ne bayan ya tafi ƙasar Burtaniya domin a yi masa tiyata.

Ya rasu ne mako ɗaya gabanin ranar 3 ga watan Satumba, 2024, ranar da zai cika shekara 53 a duniya, cewar rahoton Vanguard.

Majalisa ta ɗage zama domin karrama Sanata Ubah

Rasuwar sanatan na jam'iyyar APC ta jefa ƴan Najeriya musamman abokansa na siyasa cikin jimami da alhini.

Kara karanta wannan

Tinubu ya shiga taron FEC ana rade raɗin za a kori wasu ministoci, bayanai sun fito

A halin yanzu dai majalisar wakilai ta ƙasa ta sanar da ɗage zamanta na farko daga yau Talata zuwa gobe Laraba, 25 ga watan Satumba, 2024 domin girmama shi.

Majalisar dattawa ta tallafawa Maiduguri

A wani rahoton kuma Majalisar dattawan kasar nan ta aika tawaga ta musamman zuwa Borno domin jajanta wa gwamna Babagana Zulum kan ambaliya.

Jama'a sun shiga cikin mawuyacin hali bayan ruwa ya haura madatsar Alau, ya kuma mamaye gidaje, hanyoyi da sauran wurare a babban birnin jihar Borno.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262