Zaben Edo: 'Yan Sanda Sun Yi Karin Haske yayin da APC, PDP da LP Ke Neman Nasara

Zaben Edo: 'Yan Sanda Sun Yi Karin Haske yayin da APC, PDP da LP Ke Neman Nasara

  • Mataimakin Sufeto-Janar na ƴan sandan Najeriya, DIG Frank Mba ya bayyana cewa an samu fitowar masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamnan jihar Edo
  • Frank Mba ya bayyana gamsuwa da matakan tsaro da aka ɗauka, yana mai nuna cewa an gudanar da zaɓen cikin lumana
  • Ƴan takara 17 ne suka fafata a zaɓen na ranar Asabar, 21 ga watan Satumban 2024 inda jam’iyyun APC, PDP da LP ke kan gaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Edo - Mataimakin Sufeto-Janar na ƴan sanda (DIG) Frank Mba ya bayyana cewa jama’a sun fito domin kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan jihar Edo.

Frank Mba, wanda ke kula da ayyukan tsaro a zaɓen, ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Asabar, 21 ga Satumba, 2024.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: Dan takarar PDP ya fadi wanda zai yi nasara da gagarumin rinjaye

Frank Mba ya magantu kan zaben Edo
Frank Mba ya ce mutane sun fito zabe a Edo Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Facebook

Me ƴan sanda suka ce kan zaɓen Edo?

DIG Frank Mba ya bayyana cewa tawagarsa ta ziyarci rumfunan zaɓe da dama a faɗin jihar, inda suka lura da ɗumbin masu kaɗa kuri’a da suka fito zaɓen, cewar rahoton jaridar TheCable.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai, kuma ya bayyana cewa an samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri'a a wasu rumfunan zaɓen.

"Mun ziyarci rumfunan zaɓe da dama kuma ya zuwa yanzu, mun ga jama'a sun fito da dama."

- Frank Mba

Frank Mba ya yi magana kan yanayin tsaro

Game da samar da tsaro, DIG Frank Mba a bayyana gamsuwa kan yadda zaɓen ya gudana baki ɗaya, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar.

"A gare mu babban abin da muka damu da shi, shi ne batun tsaro a lokacin kowane zaɓe, kuma ya zuwa yanzu na gamsu da rahotannin da na ke samu.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: Oshiomole ya yi martani kan zargin APC na siyan kuri'u

- Frank Mba

Mataimakin Sufeto-Janar na ƴan sandan ya kuma tabbatarwa da jama’a cewa ƴan sanda na magance duk wasu ƙananan matsalolin tsaro da suka taso.

Dan takarar PDP ya magantu

A wani labarin kuma, kun ji cewa ɗan takarar jam'iyyar PDP a zaɓen gwamnan jihar Edo, Asue Ighodalo ya ce shi ne zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaɓen.

Asue Ighodalo ya bayyana hakan ne bayan ya kaɗa ƙuri'arsa a rumfar zaɓensa da ke makarantar firamare ta Indinrio a Okaigben Ewohomi cikin ƙaramar hukumar Esan ta Kudu maso Gabas ta jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng