Zaben Edo: PDP Ta Bukaci IGP Ya Janye Babban Jami'in 'Yan Sanda, Fadi Dalili

Zaben Edo: PDP Ta Bukaci IGP Ya Janye Babban Jami'in 'Yan Sanda, Fadi Dalili

  • Jam'iyyar PDP ta yi kira ga shugaban ƴan sandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun da ya janye mataimakinsa na shiyya ta bakwai
  • PDP ta zargin cewa AIG Benneth Igwe ya haɗa baki da jam'iyyar APC domin ba ƴan daban jam'iyyar kariya su tayar da hargitsi
  • Jam'iyyar ta buƙaci Kayode Egbetokun da ya gaggauta cire shi daga aikin zaɓen domin kaucewa samun rikici a jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Edo - Jam'iyyar PDP ta yi kira da babban murya ga babban sufeton ƴan sanda na ƙasa, Kayode Egbetokun kan zaɓen gwamnan jihar Edo.

Jam'iyyar PDP ta buƙaci Kayode Egbetokun da ya gaggauta janye mataimakin babban sufeton ƴan sanda (AIG) na shiyya ta bakwai, Benneth Igwe, daga aikin zaɓen Edo domin kaucewa tayar da hargitsi.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: 'Yan sanda sun yi gargadi ana dab da fara kada kuri'a

PDP ta yi kira ga IGP
PDP ta bukaci IGP ya janye babban jami'in 'yan sanda daga aikin zaben Edo Hoto: @OfficialPDPNig, @PoliceNG
Asali: Twitter

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jam'iyyar ta sanya a shafinta na X mai ɗauke da sa hannun sakataren yaɗa labaranta na ƙasa, Debo Ologunagbo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me yasa PDP ke son IGP ya cire Igwe?

PDP ta buƙaci hakan ne biyo bayan zarge-zargen da ake yi cewa AIG Benneth Igwe ya haɗa baki da APC domin ba ƴan daban APC kariya ta yadda za su farmaki cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.

PDP ta yi zargin cewa AIG ɗin ya yi wani zama da wasu jami'an ƴan sanda domin ganin an aiwatar da wannan shirin.

"Saboda haka jam’iyyarmu ta na kira ga IGP da ya gaggauta kiran AIG zuwa Abuja domin ci gaba da zamansa a Jihar Edo tuni ya janyo fargaba a jihar."
"Dole ne AIG ya fito ya yi magana tare da wanke kansa kan wannan babban zargin da ake yi masa."

Kara karanta wannan

"Akwai matsala": Gwamna ya gano mugun shirin da ƴan daba ke yi ana dab da fara zaɓe

"Jam’iyyar PDP ta yabawa matasan jihar Edo bisa taka-tsan-tsan da jajircewar da suka nuna wajen ganin cewa ba a karkatar da abin da jama'a suke so ba a wannan zaɓen."

- Debo Ologunagba

Rigima ta ɓarke a zaɓen Edo

A wani labarin kuma, kun ji cewa sabuwar rigima ta barke a gundumar Orhionmwon da ke karamar hukumar Orhionmwon ta Edo yayin da ake gudanar da zaben gwamnan jihar.

Rahotanni sun bayyana cewa an dakatar da kada kuri'a a rumfa ta daya a gundumar bayan jami'an INEC sun manta da takardar rubuta sakamakon zabe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng