Daga Ƙarshe, An Bayyana Yawan Tirelolin Shinkafar da Shugaba Tinubu Ya Turo Kano

Daga Ƙarshe, An Bayyana Yawan Tirelolin Shinkafar da Shugaba Tinubu Ya Turo Kano

  • Gwamnatin tarayya ta tura tallafin tirela 19 na shinkafa zuwa Ƙano domin a rabawa talakawa da ke cikin yunwa
  • Maryam Shetima, ƴar kwamitin rabon tallafin abincin ce ta bayyana haka ranar Litinin, 16 ga watan Satumba, 2024
  • Ta ce kwamitin ya gama tsare-tsaren da ya kamata domin tabbatar da kayan abincin sun isa hannun mabuƙata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Bola Tinubu ta bai wa jihar Kano tallafin tireloli 19 na shinkafa a wani mataki na rage yunwa a tsakanin al'umma.

Ɗaya daga cikin ƴan kwamitin da gwamnati ta kafa domin sa ido kan yadda za a raba tallafin, Maryam Shetima ce ta bayyana haka ranar Litinin.

Kara karanta wannan

Kwanaki 3 kafin zabe, gwamnan Edo ya raba kyautar Naira biliyan 1 ga mata

Tallafin shinkafar Bola Tinubu.
Gwamnatin tarayya ta ba Kano tallafin tirela 19 na shinkafa Hoto: @aonanuga1956
Asali: Twitter

A wata hira da Arise tv, Maryam Shettima ta tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta aiko tirela 19 maƙare da buhunan shinkafa zuwa Kano.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Maryam Shetty da aka cire sunanta daga jerin ministoci gabanin majalisar dattawa ta tantance ta, ta tabbatar cewa kwamitin ya yi tsari yadda sakon zai isa ga talakawa.

Gwamnatin Tinubu ta ba Kano tirela 19

A rahoton da Premium Times ta tattara, Maryam ta ce:

"Tirela 19 na shinkafa aka ba Kano, ban da tabbacin adadin da aka tura sauran jihohi amma dai na san wannan somin taɓi ne. Ku duba an ba Kano tirela 19, nawa kuke tunanin za a turawa sauran jihohi 36."

Ta ba da tabbacin cewa bisa tsarin da kwamitin ya yi, wannan kayan tallafi za su isa ga talalakawa da marasa galihu a faɗin kananan hukumomin Kano.

Kara karanta wannan

Ana murnar kisan ubangidan Bello Turji, gwamna ya ƙara tona badaƙalar ministan Tinubu

Sai dai Maryam ba ta ce komai ba game da girman buhunan shinkafar, wanda zai iya zama kilo 10, 25 ko 50.

Jibrin ya koka kan karkatar da tallafi a Kano

A kwanakin baya mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin ya nuna damuwa kan yadda wasu ɗaiɗaiku ke karkatar da tallafin Bola Tinubu da aka turo Kano domin amfanin kansu.

Sanata Barau Jibirin, mai wakiltar Kano ta Arewa, shi ne shugaban kwamitin rabon kayan agaji na gwamnatin tarayya a Kano.

Yayin da take amsa tambaya game da yiwuwar karkatar da shinkafar, Maryam Shettima ta ba da tabbacin cewa mambobin kwamitin za su yi adalci wajen rabon.

Ta ce babu alfarma ko son zuciya, kwamitin zai yi bakin ƙoƙarinsa wajen raba kayan abincin ga mabukata ba tare da nuna banbancin jam'iyya ba.

Gwamnan Kano ya ba Borno tallafin N100m

A wani rahoton kuma gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kai tallafin Naira miliyan 100 ga al'ummar Maiduguri da ambaliyar ruwa ta rutsa da su.

Kara karanta wannan

NMA ta hango wata matsala bayan ambaliya a Maiduguri, ta ba da mafita

Gwamnatin Kano ta bayar da tallafin ne bayan da ta kai ziyarar duba irin barnar da ambaliyar ta yi tare da jajantawa al'ummar Borno.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262