Jerin Manya da DSS Ta Cafke da Cin Zarafi da Suka Jawo Cece Kuce a cikin Mako

Jerin Manya da DSS Ta Cafke da Cin Zarafi da Suka Jawo Cece Kuce a cikin Mako

Abuja - Yan Najeriya da dama sun caccaki hukumar tsaro ta farin kaya, DSS kan cin zarafin al'umma.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

A cikin mako daya, hukumar ta kama manyan mutane da dama a kasar tare da cin zarafin al'umma.

Ana zargin DSS da kame da kuma cin zarafin mutane babu ka'ida
Jerin mutane da DSS da cin zarafinsu da ake ta cece-kuce. Hoto @OfficialDSSNG.
Asali: Twitter

Ayyukan DSS a cikin mako guda

Bayan dira a ofishin SERAP, hukumar ta kuma cafke shugaban NLC, Joe Ajaero da wasu mutane. Bayan dira a ofishin SERAP, hukumar ta kuma cafke shugaban NLC, Joe Ajaero da wasu mutane.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit Hausa ta duba mutanen da DSS ta kama da ake ganin cin zarafi ne.

Kara karanta wannan

Jama'a sun razana bayan jami'ai da bindigu sun yi awon gaba da kantoma a Kano

1. Joe Ajaero

Hukumar DSS ta cafke shugaban kungiyar kwadago, Joe Ajaero a filin tashi da saukar jiragen sama.

Kama Ajaero ya jawo ka-ce-na-ce da ake ganin cewa ana neman rufe bakin kungiyar ne bayan karin farashin mai.

Daga bisani, kungiyar ta yi barazana tare da ba gwamnati wa'adi zuwa 12 na dare kafin aka sake Ajaero mintuna kafin wa'adin ya cika.

2. Omoyele Sowore

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta kama tsohon dan takarar shugaban kasar Najeriya, Omoyele Sowore.

An ce jami'an DSS sun cafke Sowore lokacin da ya duro kasar a filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Lagas.

Rahotanni sun ce kama Sowore ba zai rasa nasaba da kiran da ya yi na 'yan kasar nan su gudanar da zanga zangar adawa da gwamnati ba.

3. Dr. Abubakar Alkali

Wani lauya a Abuja, Deji Adeyanju ya tabbatar da cewa DSS ta cafke wani malami a Jami'ar Abuja (Baze).

Kara karanta wannan

Girma ya fadi: Basarake ya shiga matsala, ana zarginsa da sace matashi da karbar N2.5m

Adeyanju ya ce hukumar ta kama malamin ne kan zargin goyon bayan zanga-zangar da aka yi a farkon watan Agustan 2024.

Rahotanni sun tabbatar cewa daga bisani hukumar ta wuce da Dr. Alkali zuwa jihar Sokoto.

4. Mamaye ofishin SERAP

A makon da ya gabata ne hukumar DSS ta mamaye ofishin SERAP bayan yi mata barazana kan karin farashin man fetur.

SERAP ta ce jami'an sun bukaci ganawa da daraktocinta bayan mamaye ofishin nasu ba bisa ka'ida ba inda ta bukaci Bola Tinubu ya umarce su da su fice daga ofishin.

5. Cin zarafi a Kano

An yi ta yada faifan bidiyo inda aka gano jami'an hukumar DSS na cin zarafin wasu mutane a birnin Kano.

Abba Hikima ya ce jami'an sun harbi wani matashi tare da cin zarafin mata da kuma dattawa a unguwar Badawa.

Ana zargin jami'an sun dauki matakin ne domin hana kwatar unguwa bin kofar gidan wani mai gidansu.

Kara karanta wannan

Shirin zanga zangar Oktoba: DSS ta cafke ɗan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore

Abba Bichi ya musanta satar kudin mahaifinsa

Kun ji cewa dan tsohon daraktan hukumar DSS, Yusuf Magaji Bichi ya ƙaryata jita-jitar cewa ya sace kudin mahaifinsa.

Abba Bichi ya ce an yi ta yada cewa ya saci $2m kuma ya tsere ya bar kasa inda ya ce babu kamshin gaskiya a labarin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.