Hotuna: Fursunoni 274 Sun Tsere daga Gidan Yarin Maiduguri bayan Ambaliyar Ruwa

Hotuna: Fursunoni 274 Sun Tsere daga Gidan Yarin Maiduguri bayan Ambaliyar Ruwa

  • Hukumar kula da gidan yarin Najeriya (NCoS) ta bayyana cewa fursunoni 274 ne suka tsere bayan ambaliyar ruwa ta mamaye Maiduguri
  • Hukumar ta ce fursunonin sun tsere ne lokacin da ake kwashe su daga matsakaiciyar cibiyar tsaro ta Maiduguri bayan rushewar katangarta
  • Sai dai hukumar ta ba da tabbacin cewa tana adane da bayanan fursunonin harma da shacin yatsunsu kuma za a kamo su nan ba da jimawa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Borno - Hukumar da ke kula da gidajen yarin Najeriya ta ce fursunoni 281 sun tsere daga matsakaiciyar cibiyar tsare masu laifi da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Hukumar ta bayyana cewa fursunonin sun tsere a lokacin da ake kwashe su daga gidan cibiyar tsaron bayan afkuwar ambaliyar ruwa a jihar.

Kara karanta wannan

Ambaliyar Maiduguri: Mutanen da aka ceto daga gidaje sun haura 3,600

Gwmnati ta yi magana kan fursunonin da suka tsere a Maiduguri
Gwamnati ta fitar da hotunan fursunonin da suka tsere daga cibiyar tsaro ta Maiduguri. Hoto: @CorrectionsNg
Asali: Twitter

Ambaliyar ruwa a birnin Maiduguri

Kakakin hukumar NCoS, Umar Abubakar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a Abuja, ranar Lahadi kamar yadda jaridar Daily Trust ta rahoto.

Ambaliyar ruwan da ta mamaye sassa daban-daban na Maiduguri ta shafi mutane sama da miliyan guda, tare da haddasa mutuwar mutane akalla 30.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ta dukufa wajen gudanar da ayyukan ceto, inda ta ceci mutane sama da 400 da ambaliyar ruwa ta rutsa da su.

Fursunoni 274 sun tsere a Maiduguri

Umar Abubakar ya ce hukumar ta adana bayanan fursunonin da suka tseere tare da shacin yatsunsu.

The Punch ta rahoto Mista Umar ya ce:

“Ambaliyar ta rusa katangar gidan gyaran halin, ciki har da matsakaiciyar cibiyar tsaro ta Maiduguri (MSCC) da gidajen ma’aikata da ke cikin birnin.

Kara karanta wannan

Bayan ambaliya ta kashe mutum 37, gwamnati ta ba da umarni kan madatsar Alau

“Bayan jami’an hukumar NCoS tare da goyon bayan wasu hukumomin tsaro sun kwashe fursunonin zuwa wani wuri mai tsaro na daban, an gano fursunoni 281 sun tsere.
“Yanzu haka, san sake cafko jimillar fursunoni bakwai kuma an mayar da su gidan yarin, yayin da ake kokarin nemo sauran domin mayar da su inda suke a tsare."

Fursunoni sun tsere a Suleja

A wani labarin, mun ruwaito cewa hukumar da ke kula da gidajen gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta bayyana cewa fursunoni 69 suka tsere daga gidan gyaran hali na Suleja a jihar Neja.

Hukumar kula da gidajen yarin ta ce ta zabi bayyana bayanan fursunonin ne domin ganin an kamo su tare da mayar da su gidan yarin cikin gaggawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.