Gobara Ta Lakume Kasuwar Katako Kurmus, an Fadi Asarar da Aka Yi

Gobara Ta Lakume Kasuwar Katako Kurmus, an Fadi Asarar da Aka Yi

  • Mutane da dama sun tafka asara bayan gobara ta tashi a kasuwar katako ta Itamaga a Ikorodu da ke jihar Lagos
  • Daraktan hukumar ba da agajin gaggawa, Nosa Okunbor ya ce gobarar ta jawo mummunan asara na miliyoyi a jihar
  • Okunbor ya ce an tabbatar da cewa matsalar wutar lantarki ne ya jawo gobarar kafin nasarar dakile ta cikin gaggawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Lagos - An shiga wani irin yanayi bayan gobara ta kama a wata kasuwar katako da ke jihar Lagos.

Gobarar ta kama ne da safiya a kasuwar Itamaga da ke Ikorodu wanda ya yi sanadin asarar miliyoyi.

Gobara ta kama kasuwar katako a jihar Lagos
Mutane da dama sun tafka asara bayan gobara ta kona kasuwar katako a Lagos. Hoto: LASG Fire and Rescue Service.
Asali: Facebook

Gobara ta lakume kasuwar katako a Lagos

Kara karanta wannan

Sokoto: Mummunar gobara ta babbake ofisoshi 6 a hedikwatar 'yan sandan Najeriya

Daraktan hukumar ba da agajin gaggawa a jihar, Nosa Okunbor shi ya tabbatar da haka, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Okunbor ya ce gobarar ta fara da misalin karfe 3.00 na dare wanda ta yi sanadin lakume shaguna makare da dukiyoyi.

Yayin da masu ba da taimakon gaggawa suka zo, Okunbor ya ce sun gano cewa gobarar ta kama ne saboda matsalar wutar lantarki.

Ya ce zuwan masu ba da agajin da kuma jami'an hukumar kashe gobara ya yi tasiri wurin dakile matsalar, cewar rahoton Tribune.

An gano musabbabin gobarar a Lagos

"Bayan zuwan masu ba da agaji, an gano wutar lantarki ta jawo gobarar da ta lakume shaguna da dama."
"An gudanar da bincike mai zurfi inda aka gano cewa matsalar wutar lantarki ne daga wani bangare ya jawo."

Kara karanta wannan

Bayan ambaliya a Borno da Bauchi, an shiga fargaba a garuruwan Yobe

"Gudunmawar da hukumomi da hukumar kashe gobara ta jihar Lagos sun tabbatar da kawo karshen gobarar."

Nosa Okunbor

Jarumin fina finai ya kwanta dama

Kun ji cewa masana'antar shirya fina-finan Nollywood a Najeriya ta shiga jimami bayan rasuwar jarumi, Shina Sanyaolu a jihar Lagos.

Marigayin ya rasu ne a ranar Laraba 11 ga watan Satumbar 2024 duk da ba a bayyana silar mutuwar jarumin ba.

Jaruman fina-finan Nollywood da dama sun tura sakon ta'aziyya inda suka tabbatar da cewa Shina mutumin kirki ne.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.