Ana Dab da Zabe Gwamna Ya Yi Sababbin Nade Nade 300 a Gwamnatinsa

Ana Dab da Zabe Gwamna Ya Yi Sababbin Nade Nade 300 a Gwamnatinsa

  • Gwamnan jihar Ondo da ke yankin Kudu maso Yammacin Najeriya, Lucky Aiyedatiwa ya sake zaɓo wasu mutane ya ba su muƙamai a gwamnatinsa
  • Gwamnan ya naɗa sababbin hadimai mutum 344 waɗanda za su riƙa taimaka masa wajen gudanar da mulkin jihar
  • Sababbin hadiman waɗanda aka zaɓo daga ƙananan hukumomi 18 na jihar sun haɗa da mataimaka na musamman da manyan mataimaka na musamman

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Ondo - Gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya yi sababbin naɗe-naɗe a gwamnatinsa.

Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya amince da naɗa ƙarin hadimai 344 a matsayin mataimaka na musamman da kuma manyan mataimaka na musamman.

Gwamnan Ondo ya nada hadimai
Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya sake nada hadimai Hoto: Hon. Lucky Orimisan Aiyedatiwa
Asali: Facebook

Jaridar The Nation ta rahoto cewa hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaransa, Ebenezer Adeniran.

Kara karanta wannan

Gwamna ya fallasa yadda shugaban al'umma ya karbi kudi aka hallaka mutane a yankinsa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Aiyedatiwa ya nada hadimai

Jaridar The Guardian ta ce naɗe-naɗe sun haɗa da manyan mataimaka na musamman guda 28 da mataimaka na musamman guda 316.

A cewar sanarwar, Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya yi naɗe-naɗen ne domin ci gaba da ƙoƙarin inganta sha’anin mulki da matso da gwamnati kusa da al'ummar jihar.

Sanarwar ta ce naɗe-naɗen sun shafi ƙananan hukumomi 18 da kuma mazaɓu 203 da ke jihar.

Gwamna Lucky Aiyedatiwa, a cikin sanarwar, ya buƙaci sababbin hadiman da aka naɗa da su yi amfani da ƙwarewarsu da sadaukar da kansu wajen yiwa al’ummar jihar hidima. 

Karanta wasu labaran kan Gwamna Aiyedatiwa

Kara karanta wannan

Jigo a APC ya ba Tinubu shawarar abin da ya kamata ya yiwa ministocinsa

Gwamna Aiyedatiwa zai biya albashin N70,000

A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamnatin jihar Ondo ƙarƙashin jagorancin Gwamna Lucky Aiyedatiwa, ta amince da biyan N70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Gwamnatin ta ɗauki wannan matakin ne biyo bayan rattaɓa hannu kan ƙudirin dokar mafi ƙarancin albashin da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng