An Samu Matsala Tsakanin Tinubu da Shettima? Hadimin Kashim Ya Magantu

An Samu Matsala Tsakanin Tinubu da Shettima? Hadimin Kashim Ya Magantu

  • An yi ta yada jita-jita cewa akwai matasala tsakanin Shugaba Bola Tinubu da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima
  • Sai dai fadar shugaban kasa ta yi magana kan rade-radin da yake yawo a yau inda ta ce babu gaskiya kan abin da ake yadawa
  • Hadimin Shettima a bangaren sadarwa, Stanley Nkwocha shi ya bayyana haka inda ya ce akwai alaka mai kyau tsakaninsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Fadar shugaban kasa ta yi magana kan rade-radin samun matsala tsakanin Shugaba Bola Tinubu da mataimakinsa.

Martanin na zuwa ne bayan zargin cewa alaka ta yi tsami tsakanin Mai girma Bola Tinubu da Kashim Shettima har ba a ga maciji.

Kara karanta wannan

2027: Shekarau zai jagoranci tawaga mai karfi domin kifar da Tinubu, sun fara shiri

Fadar shugaban kasa ta yi magana kan zargin alaka mai tsami tsakanin Shettima da Tinubu
Fadar shugaban kasa ta karyata zargin matsala tsakanin Tinubu da Shettima. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Kashim Shettima.
Asali: Facebook

Akwai matsala tsakanin Shettima da Tinubu?

Hadimin Shettima a bangaren yada labarai, Stanley Nkwocha ya ce akwai alaka mai kyau tsakanin Shettima da mai gidansa, cewar rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce an kirkiri labarin ne kawai domin hada rigima inda ya ce kwata-kwata ba abin da ke faruwa ba kenan a Aso Rock.

Nkwocha ya karyata labarin da ake yadawa inda ya ce Shettima yana mutunta Tinubu matuka.

Hadimin Shettima ya fadi alakarsu da Tinubu

"Shettima ya himmatu wurin tabbatar da ba da goyon baya ga Bola Tinubu domin samun cigaba."
"Irin goyon baya da hadin kai da Shettima ke ba Tinubu shi ya kara daidaita tsakaninsu domin kawo sauyi a gwamnatinsu."

- Stanley Nkwocha

Stanley ya yabawa Shettima duba da irin hadin kai da ya ke ba shi inda ya ce Tinubu shugaba ne wanda 'yan Najeriya ya kamata su aminta da shi.

Kara karanta wannan

"Ka yi daidai": Shekarau ya yabawa Tinubu kan nade nade, ya fadi damuwar Arewa

Ya shawarci al'umma da su guji yada jita-jita musamman irin wannan da zai kawo rudani a kasa.

Bikin ranar haihuwa: Shettima ya roki al'umma

Kun ji cewa Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ta roki yan Najeriya kan murnar zagayowar ranar haihuwarsa.

Sanata Kashim Shettima ya bukaci al'umma da su guji kashe kudi domin taya shi murnar cika shekaru 58 a duniya.

Mataimakin shugaban kasar ya bukaci masu son taya shi murnar su yi amfani da kudin wurin taimakon gidajen marayu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.