'Yan Bindiga Sun Jefa Bama Bamai a Hedkwatar Ƴan Sanda, Sun Tafka Ta'asa

'Yan Bindiga Sun Jefa Bama Bamai a Hedkwatar Ƴan Sanda, Sun Tafka Ta'asa

  • Jami'i ɗaya ya mutu da ƴan bindiga suka kai mummunan farmaki a hedkwatar ƴan sanda da ke garin Oba a jihar Anambra
  • Mai magana da yawun ƴan sandan jihar, Tochukwu Ikenga ya ce maharan sun riƙa jefa bama-baman kwalabe a wannan harin
  • Ya ce tuni jami'an tsaro da suka haɗa da sojoji, ƴan sanda da sauran dakarun hukumomin tsaro suka fara farautar maharan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Anambra - Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan aware ne sun kai hari hedikwatar ‘yan sanda da ke garin Oba karamar hukumar Idemili ta Kudu a Anambra.

Rahotannin da muka samu sun nuna cewa ƴan ta'addan sun kashe kofur na ƴan sanda a harin wanda suka kai da safiyar ranar Talata, 3 ga watan Satumba, 2024.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun jikkata matar ɗan Majalisa, sun hallaka ƴan sanda a Najeriya

Yan sanda.
Yan bindiga sun kai hari hedimwatar ƴan sanda, sun kashe kofur a Anambra Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Facebook

Mahara sun yi wa ƴan sanda ta'asa

Wata majiya ta shaidawa Daily Trust cewa maharan sun kashe kofur tare da jikkata wasu jami'an ƴan sanda da ke aiki a hedikwatar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyar ta ƙara da cewa ‘yan bindigar sun kuma kai hari a cibiyar Oba Civic Centre, har yanzu babu cikakken bayani kan dalilin kai wannan hari.

Amma harin ya zo a daidai lokacin da jagoron ƴan aware, Simon Ekpa, ya yi barazanar sa ƙafar wando ɗaya da duk wani abu da ya shafi gwamnati a Kudu Maso Gabas.

Ƴan sanda sun faɗi matakin da aka ɗauka

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da kai harin a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce tuni dakarun haɗin guiwa da suka kunshi, sojoji, jami'an tsaron fararen hula NSCDC da sauran hukumomin tsaro suka fara farautar maharan a Oba da Kewaye.

Kara karanta wannan

"Ka bi a hankali": Gwamnan PDP ya gargadi kwamishinan 'yan sanda

Kakakin ƴan sandan ya ce maharan sun buɗe wuta kan mai uwa da wabi da kuma jefa bama-baman kwalaben fetur a hedkwatar ƴan sandan, Punch ta kawo labarin.

"Abin takaicin kofur ɗaya wanda ya ji munanan raunuka a harin ya rasa ransa daga baya amma an yi nasarar kashe wutar da ta tashi da taimakon jami'an tsaro," in ji Ikenga.

Ƴan bindiga sun kai farmaki sakatariya a Anambra

A wani rahoton kun ji cewa wasu yan bindiga kimanin 30 sun dura ƙaramar hukumar Ogbaru a jihar Anambra inda suka bude wuta a sakatariya.

Rahotanni sun nuna cewa yan bindigar sun yi kone kone a karamar hukumar kafin su yi musayar wuta da yan sandan jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262