Sabuwar Zanga Zanga Ta Ɓarke a Abuja, Matasa Sun Aika Sako ga Shugaba Tinubu

Sabuwar Zanga Zanga Ta Ɓarke a Abuja, Matasa Sun Aika Sako ga Shugaba Tinubu

  • Zanga zanga ta sake ɓallewa a babban babban birnin tarayya Abuja kan karancin man fetur da ya ƙi ƙarewa a Najeriya
  • Masu zanga-zangar sun nuna takaicinsu kan yadda lamarin ke ƙara lalacewa karƙashin shugaban kamfanin NNPCL
  • Sun buƙaci Bola Ahmed Tinubu da sauran waɗanda ke riƙe da madafun iko su ɗauki mataki domin shawo kan lamarin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Dandazon mutane sun fantsama kan tituna a babban birnin tarayya Abuja domin nuna fushinsu kan matsalar ƙarancin man fetur.

Masu zanga zangar sun bukaci a tsige shugaban kamfanin mai na ƙasa (NNPCL) Mele Kyari, saboda ya gaza magance ƙarancin mai da aka jima ana fama da ita.

Kara karanta wannan

Tofa: Ƴan sanda sun bayyana Bature da ya nemi kifar da gwamnatin Tinubu a Najeriya

Masu zanga zanga.
Zanga zanga ta ɓalle a Babban Birnin Tarayya Abuja kan karancin man fetur Hoto: Pierre Favennec
Asali: Facebook

NNPCL ya koka kan ƙarancin kuɗi

Wannan zanga-zanga na zuwa ne bayan kamfanin NNPCL ya ce ɗumbin bashin da yake bin ƴan kasuwa na barazana ga wadatar mai Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A rahoton Punch, kamfanin ya ƙara da cewa ya fara shiga matsalar rashin isassun kuɗi wanda hakan ka iya daƙile ayyukansa da ƙarancin mai a ƙasa.

Yadda matasa suka yi zanga-zanga

Masu zanga-zangar sun riƙa rera waƙoƙin haɗin kai, sannan sun ɗaga kwalayen da aka rubuta, "mun gaji ƙarancin mai da surutu kan matatun mai," da sauransu.

Da yake jawabi ga manema labarai, jagoran masu zanga-zangar Aminu Abbas, ya ce yana mamakin yadda ake karancin mai a kasar da Allah ya azurta da albarkatun mai.

Ya kuma gargaɗi shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu da sauran masu rike da madafun iko su ɗauki mataki tun yanzu kafin abin ya sha ƙarfinsu.

Kara karanta wannan

DHQ ta yi martani kan batun kwace motocin sojoji da 'yan bindiga suka yi a Zamfara

Masu zanga-zanga sun aika saƙo

A rahoton Vanguard, Aminu Abbas ya ce:

"Shugaban ƙasa Bola Tinubu da sauran shugabanni, ya kamata ku tashi daga barci, lokaci ya yi da zaku ɗauki mataki, ku nuna mana kuna kishin talaka ba kishin aljihu ba.
"Muna wahala saboda ƙarancin mai, muna kokarin jurewa amma abin ba mai ƙarewa ba ne, ƙarƙashin Mele Kyari wahala kullun ƙaruwa take, babu alamar ƙarshe."

NNPCL na shirin miƙa matatu ga ƴan kasuwa

A wani rahoton kuma kamfanin man fetur na kasa ya fara neman yan kasuwa da za su iya rike wasu matatun man da ke karkashinsa.

Kamfanin NNPCL na neman yan kasuwar da za su iya kula da gyara matatun da ke Kaduna da Warri bayan sun gaza fara aiki.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262