Bayan Tafiyar Yusuf Bichi, an Bukaci Babban Jami'in Gwamnati Ya Yi Murabus

Bayan Tafiyar Yusuf Bichi, an Bukaci Babban Jami'in Gwamnati Ya Yi Murabus

  • An yiwa shugaban kamfanin man fetur na ƙasa (NNPCL), Mele Kyari, hannunka mai sanda kan jan ragamar kamfanin
  • Wani babban mamba a jam'iyyar PDP, Abdul-Aziz Na'ibi Abubakar, ya buƙaci Mele Kyari da ya yi murabus daga kan muƙaminsa
  • Abdul-Aziz ya shawarci Mele Kyari da ya yi murabus ɗin ne bayan shugabannin hukumomin DSS da NIA sun ajiye aikinsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - An buƙaci shugaban kamfanin man fetur na ƙasa (NNPCL), Mele Kyari, ya yi murabus daga kan muƙaminsa.

Wani babban mamba a jam'iyyar PDP, Abdul-Aziz Na'ibi Abubakar, ya ba shugaban na kamfanin NNPCL shawarar ya ajiye aikinsa.

An bukaci Mele Kyari ya yi murabus
An ba Mele Kyari shawara ya yi murabus Hoto: @nnpclimited
Asali: Facebook

Abdul'aziz Na'ibi Abubakar ya ba Mele Kyari wannan shawarar ne a wani rubutu da ya yi a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Yajin aiki: An samu matsala a taron da gwamnatin Tinubu za ta ya da ASUU

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugabannin DSS, NIA sun yi murabus

Shawarar da ya ba Mele Kyari na zuwa ne bayan shugaban hukumar ƴan sandan farin kaya (DSS), Yusuf Magaji Bichi da na hukumar leƙen asiri ta ƙasa (NIA), Alhaji Ahmed Rufa'i Abubakar sun yi murabus daga muƙamansu.

Bayan murabus ɗin na su, Shugaba Tinubu ya maye gurbinsu da sababbin waɗanda za su ci gaba da jan ragamar hukumomin.

A hukumar NIA, Shugaba Tinubu ya naɗa Mohammed Mohammed domin maye gurbin Alhaji Ahmed Rufa'i Abubakar.

Adeola Oluwatosin Ajayi zai jagoranci hukumar DSS bayan murabus ɗin da Yusuf Magaji Bichi ya yi a ranar, 24 ga watan Agustan 2024.

Wace shawara aka ba Mele Kyari?

Mamban na PDP ya buƙaci Mele Kyari da ya yi murabus ka da ya bari har sai ta kai ga an kunya ta shi ta hanyar sauke shi daga muƙaminsa.

Kara karanta wannan

PDP ta fara shirin hukunta tsohon sanata bayan ya kwance mata zani a kasuwa

"Yanzu saura kai, Mele Kyari. Idan kaga dama ka da ka yi murabus, ka jira har sai sun kunya ta ka."

- Abdul-aziz Na'ibi Abubakar

Atiku ya ba Tinubu shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya yi kira ga Bola Tinubu kan dawo da tallafin man fetur.

Atiku Abubakar ya ce ya kamata Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi halin maza wajen fadawa yan Najeriya cewa ya dawo da tallafin mai maimakon boye boye da yake.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng