A Kai Zuciya Nesa: Matashi Ya Yi Yunkurin Aikata Sheke-Kai Bayan Bashi Ya Masa Katutu

A Kai Zuciya Nesa: Matashi Ya Yi Yunkurin Aikata Sheke-Kai Bayan Bashi Ya Masa Katutu

  • ‘Yan sandan jihar Anambra sun ceto wani matashi daga aikata sheke-kai bayan bashi ya masa katutu
  • Rahoto ya bayyana dalilin da yasa matashin ya shiga tashin hankali har ya kai ga daukar mummunan mataki
  • Ba wannan ne karon farko da ake samun matasa na daukan munanan matakin da ke kai wa ga rasa rai ba

Jihar Anambra - Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta ce ta ceto wani matashi mai shekaru 27, Alozie John daga yunkurin kawo karshen rayuwarsa a unguwar Umunnachi da ke karamar hukumar Dunukofia.

Matashin makiyayi dan asalin Isielu ta jihar Ebonyi an ce ya yi yunkurin sheke kansa ne bayan da ya dabaibaye kansa da bashin N1.2m.

'Yan sanda sun ceto matashi zai yi sheke-kai
Yadda aka ceto daga aikata aikata sheke-kai | Hoto: Adekunle Ajayi
Asali: Getty Images

Yadda aka gano zai yi sheke-kai

A wata sanarwar da rundunar ‘yan sandan ta fitar a ranar Asabar ta bakin mai magana da yawun hukumar, SP Tochukwu Ikenga ta ce, an kai ga ceto shi bayan ganin wata hirarsa ta manhajar WhatsApp.

Kara karanta wannan

Bidiyon matasa sun farmaki dan takarar gwamna bayan hukunci a Kotun Koli

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar Ikenga:

“A ranar 23 ga watan Agusta, rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta ceto wani matashin da ya yi yunkurin yin sheke-kai. An ceto shi, an ba shi agajin maganin gaggawa kana an ajiye shi a wuri killatacce don zuba masa ido.”

Kasuwar kajin gona sun tunzura matashi

A cewar rundunar, bashi ne ya dabaibaye matashin, wanda aka ce ana binsa kusan N1.2m na kaji da yake kasuwanci da kiwonsu, Punch ta ruwaito.

A halin da ake ciki, tuni rundunar ta kira mahaifiyar matashin, kuma an ce tana ba da hadin kai wajen tabbatar da an kai ga tushen bincike.

Halin da matashin ke ciki a yanzu

Hakazalika, an ce an ajiye matashin a wuri mai aminci tare da zuba masa ido don tabbatar da bai kuma aiwatar da wani nau’in cutar da jiki ba, rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

Daga karbar kudi ta zama budurwar wasa a makaranta, an ga gawar daliba a bola

Da kansa, matashin ya ce yana harkallar kaji ne kuma ya sha guba amma bai samu nasarar sadawa ga ubangijinsa ba.

Wata aika-aikar da tsageru suka aikata

A wani labarin, akalla mutane 10 ne suka rasa rayukansu a wani hari da aka kai kauyukan Mandung-Mushu da Kopnanle na karamar hukumar Bokkos ta jihar Plateau.

Rahoton da muka samo ya ce, an fara kai harin ne da misalin karfe 10 na daren Juma’a bayan mutanen kauyen suka gama harkokinsu na rana suka shiga bacci da dare.

Wata majiya ta shaida wa jaridar Daily Trust cewa, harin ya haifar da tashin hankali a cikin garin na Bokkos da kewaye.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.