Ana Tsadar Rayuwa, An Kama Dattijo Mai Shekaru 62 Yana Haɗa Kuɗin 'Bogi'

Ana Tsadar Rayuwa, An Kama Dattijo Mai Shekaru 62 Yana Haɗa Kuɗin 'Bogi'

  • Rundunar yan sanda a jihar Bauchi sun samu nasarar cafke wani dattijo mai shekaru 62 da ake zargi da hada kuɗin ganye
  • Rahotanni sun nuna cewa an kama mutumin ne yayin da ya shiga garin Bauchi bayan ya fito daga jihar Filato a cikin motar haya
  • Rundunar yan sanda ta dauki matakin magana da babban bankin Najeriya CBN domin gano sahihancin kudin da mutumin ya haɗa

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Bauchi - Rundunar yan sandan Najeriya a jihar Bauchi ta kama wani dattijo da ake zargi da hada jabun kuɗi.

Kakakin yan sanda na jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil ya bayyana matakin da suka dauka domin gano sahihancin kudin.

Kara karanta wannan

An kama mutumin da yake saida sassan jikin ɗan Adam, an same shi da kan wata mata

Yan sanda
An kama mai hada kudi a Bauchi. Hoto: Nigerian Police Force Bauchi State Command
Asali: Facebook

Legit ta tatttaro yadda aka kama mutumin ne a cikin wani sako da rundunar yan sanda ta wallafa a shafinta na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dattijo ya haɗa kudin ganye a Bauchi

Rundunar yan sanda ta bayyana cewa wani dattijo ya shiga motar haya daga jihar Filato zuwa Bauchi kuma ya haɗa kudin ganye a yayin da suke tafiya.

Shaidar gani da ido ya tabbatar da cewa mutumin ya yi amfani da takardu ne yayin haɗa jabun kudin a cikin motar hayar.

Bauchi: Yadda aka kama mai hada kudi

Rundunar yan sanda ta bayyana cewa wani mutum ne a cikin motar ya fallasa dattijon a lokacin da suka sauka a garin Bauchi.

Rahoto ya nuna cewa suna isowa garin Bauchi daga Filato sai wani a cikin motar ya nemi yan sanda fada musu abin da mutumin ya yi.

Kara karanta wannan

An shiga jimami a Arewacin Najeriya, mata da miji da 'ya'yansu 5 sun mutu bayan cin rogo

Yan sanda za su tuntubi CBN

Rundunar yan sanda ta bayyana cewa a halin yanzu za ta tuntubi babban bankin Najeriya domin gano sahihancin kudin da ake zargi mutumin ya haɗa.

An zargi mutumin mai suna Tahir Ahmed da hada kudi yan Naira dubu dubu ne yayin da suke tafiya a cikin motar haya.

An kama mata da miji kan jabun kudi

A wani rahoton, kun ji cewa jami'an 'yan sanda sun kama wasu ma'aurata, Olamilekan da Oluwayemisi Oludare kan zargin raba jabun kudi

Olamilekan ya ce suna siyarwa 'yan canji da jabun kudin waje yayin da matarsa ke rabawa kwastamoni jabun naira ta san'ar POS.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng