"Ko Mutum 1 ba a Kashe Lokacin Zanga Zanga ba," Inji Rundunar 'Yan Sandan Kano

"Ko Mutum 1 ba a Kashe Lokacin Zanga Zanga ba," Inji Rundunar 'Yan Sandan Kano

  • An samu rahotanni daga jama'a da hotunan da ke yawo a kafafen sada zumunta na mutuwar wasu mutanen Kano lokacin zanga-zanga
  • Amma a yau Litinin, rundunar 'yan sandan Kano ta ce babu ko mutum guda da ya rasu ko aka harba a yayin nuna adawa da manufofin gwamnati
  • Wannan ya zama amsa kuwwar Sufeta Janar na 'yan sanda da ya musanta cewa babu jami'in tsaron da ya yi harbi yayin zanga zangar

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Rundunar 'yan sandan Kano ta hakikance kan cewar babu mutumin da harbin bindiga ya yi sanadiyyar rasuwarsa yayin zanga zanga.

Kara karanta wannan

Hauhawar farashi: Abba Gida Gida ya ji koken jama'a, gwamna ya sa labule da 'yan kasuwa

Kwamishinan 'yan sandan jihar, Salman-Dogo Garba ne ya bayyana haka ga manema labarai a zantawarsa da su a ofishin 'yan sandan Kano.

Yan sanda
Rundunar 'yan sandan Kano ta musanta kashe masu zanga zanga Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa kalaman kwamishinan na zuwa duk da an samu jama'ar da su ka tabbatar da rasuwar yan uwansu saboda harbin bindiga a lokacin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Ba mu da rahoton mutuwar kowa' - Yan sanda

Rundunar 'yan sandan Kano ta tara manema labarai inda ta musanta cewa akwai jami'inta da ya harbi masu zanga zanga a makon da ya gabata a jihar, aminiya ta ruwaito wannan.

Kwamishinan yan sandan Kano, CP Salman Dogo da ya bayyana haka ya ce a dukkanin rahoton da su ka samu, babu inda aka ce an kashe wani ko wata.

'Yan kasar nan sun yi fitar dango domin zanga-zangar adawa da yadda gwamnati ta barsu cikin talauci da matsin rayuwa, inda daga bisani lamarin ya koma tashin hankali.

Kara karanta wannan

An samu sabanin tsakanin 'yan sanda da rundunar sojoji a kan harbin 'yan zanga zanga

Sojoji sun tabbatar da harbin masu zanga-zanga

A baya mun ruwaito cewa rundunar sojoji ta kasa ta tabbatar harbin wasu daga cikin masu zanga-zanga har ta jawo asarar ran wani matashi a Samaru da ke Zaria, jihar Kaduna.

Wannan tabbaci na zuwa bayan rundunar 'yan sandan kasar nan, ta bakin babban Sufeto, Kayode Egbetokun ta karyata cewa an samu harbe-harben masu zanga zanga a kasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.