Ranar Ƙarshe: Masu Zanga Zanga Sun Sake Fantsama Kan Tituna, Ƴan Sanda Sun Ankara

Ranar Ƙarshe: Masu Zanga Zanga Sun Sake Fantsama Kan Tituna, Ƴan Sanda Sun Ankara

  • Masu zanga zanga sun sake tururuwa a kan tituna a babban birnin tarayya Abuja yau Asabar, 10 ga watan Agusta, 2024
  • Tuni dai ƴan sanda suka ƙara tsaurara tsaro a kwaryar birni tun ranar Jumu'a saboda masu zanga-zanga na shirin rufewa da gagarumin tattaki
  • Da misalin karfe 7:00 na safiya matasa suka fito zanga-zanga ta ƙarshe a Abuja kamar yadda suka tsara tun farko

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Bayan lafawa na ɗan taƙaitaccen lokaci, masu zanga zanga sun sake komawa kan tituna a birnin tarayya Abuja yau Asabar, 10 ga watan Agusta. 2024.

Zanga-zangar wacce a baya aka dakatar da ita saboda samamen da jami'an tsaro suka kai gidaje da kame masu jagorantar zanga-zangar, yanzu haka tana ci gaba da gudana.

Kara karanta wannan

Jerin ƙasashe 4 da zanga zanga ta kawo sauyin gwamnati a nahiyar Afirka

Masu zanga-zanga da ƴan sanda.
Masu zanga zanga sun sake fitowa yayin da aka tsaurara tsaro a Abuja Hoto: @EiENigeria, @rrslagos767
Asali: Twitter

Jaridar Punch ta tattaro cewa a ranar 1 ga watan Augusta, 2024 ƴan Najeriya suka fara zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa kuma a yau ake sa ran karkare ta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda suka tsara tun farko, zanga-zangar za ta ɗauki tsawon kwanaki 10 kuma a yau jagororin da suka shirya gagarumin tattaki na mutane miliyan 1 a faɗin Najeriya.

Ƴan sanda sun ɗauki mataki

Domin shiryawa wannan gagarumin tattaki, tun ranar Jumu'a hukumomi suka girke dakarun tsaro a kewayen musamman wurare a kwaryar birnin Abuja.

Haka kuma a dandalin Eagles Square, an samu karuwar adadin jami’an tsaro da ke jibge a wurin saboda zanga-zangar ranar ƙarshe, Daily Trust ta rahoto.

Wannan dai wani sauyi ne wanda ba a ga irinsa ba a kwanaki uku da suka gabata, kwanakin da masu zanga-zanga suka huta ba su fito kan tituna ba.

Kara karanta wannan

Jagora a APC ya dauko hanyar dakile zanga zanga, ya tura sako ga mai tunzura matasa

Masu zanga-zanga sun tura saƙo

A yau Asabar, masu zanga-zangar, wadanda suka fara fitowa tun da karfe 7 na safe, sun yi ta maimaita "a kawo karshen yunwa" da "A dawo mana da tallafin man fetur," da dai sauransu.

Polan ta roki Njeriyata sakin ƴan ƙasarta

A wani rahoton kuma ƙasar Poland ta roƙi Najeriya ta haƙura da saki ƴan ƙasarta da aka kama da laifin ɗaga tutocin Rasha lokacin zanga-zanga a Kano.

Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar, Jakub Wisniewski ya ce ƴan Poland bakwai da aka kama sun aikata laifin ne cikin jahilci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262