Mutane 62 Sun Mutu Yayin da Jirgin Sama Ya Yi Mummunan Haɗari, Bidiyo Ya Fito

Mutane 62 Sun Mutu Yayin da Jirgin Sama Ya Yi Mummunan Haɗari, Bidiyo Ya Fito

  • Wani jirgin sama ɗauke da fasinjoji 62 ya yi haɗari a kusa da Sao Paulo a kasar Brazil ranar Jumu'a, 9 ga watan Agusta, 2024
  • Rahotanni sun bayyana jirgin ya faɗo ne a kusa da wani gida kuma duka mutane 62 da ke ciki sun mutu
  • Bidiyoyin da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda jirgin ya faɗo ƙasa ba zato ba tsammani

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sao Paulo, Brazil - Wani jirgin sama da ya ɗauko fasinjoji 62 ya yi haɗari ranar Jumu'a, 9 ga watan Agusta, 2024 a kusa da birnin Sao Paulo na kasar Brazil.

Rahotanni sun nuna cewa jirgin ya taso ne daga filin sauka da tashin jiragen sama na Cascavel da nufin zuwa Sao Paulo amma ya faɗo a kusa da wani gida.

Kara karanta wannan

Kaico: Ƴan bindiga sun hallaka basarake, sun yi awon gaba da mata da ƙananan yara

Jirgi ya yi haɗari a Brazil.
Jirgin sama mai ɗaukar fasinjoji ya yi hatsari a ƙasar Brazil Hoto: JurgaR
Asali: Getty Images

Brazil: Fasinjoji nawa ne a jirgin?

A rahoton da BBC ta tattaro, duka fasinjoji 62 da jirgin ya ɗauko sun mutu sakamakon hatsarin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamfanin sufurin jiragen sama na VoePass, masu jirgin da ya yi hatsarin sun bayyana cewa ya ɗauko mutane 58 da ma'aikata huɗu, a cewar rahoton APN News.

Al Jazeera ta ruwaito cewa gida daya ne kaɗai da ke wajen birnin Sao Paulo ya lalace a yankin da jirgin ya fado amma babu daya daga cikin mazauna wurin da ya jikkata.

Yadda jirgin ya faɗo a Sao Paulo

Wani faifan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta ya nuna jirgin yana jujjuyawa a lokacin da ya yo ƙasa kafin daga bisani ya faɗi.

Lamarin dai ya haifar da wata babbar gobara, inda hayaki ya turnuke daga wani abu da ake ganin kamar tulun jirgin ne a kusa da gidajen da al'umma ke ciki a gefen birni.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Sojoji cun ci karo da gomman matasa a cikin mota, sun ɗauki mataki

Shugaban Brazil ya yi ta'aziyya

Shugaban kasar Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva, ya bayyana cewa da alama dukkan mutanen da ke cikin jirgin sun mutu.

"Labari mara daɗi, ina jajanta wa iyalai da abokan wadanda ibtila'in ya rutsa da su," in ji shi.

An yi mummunan hatsarin mota a Zaria

A wani rahoton kuma jama'a sun shiga tashin hankali a yankin Gwargwaje, a karamar hukumar Zaria bayan motoci biyu sun yi karo da juna.

Shugaban hukumar kare afkuwar hadurra a Kaduna, Kabir Nadabo ya bayyana cewa mutum 11 sun rasu nan take.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262