Sunayen Jihohi da Bayanan 'Yan Siyasan Arewa da Ake Tuhuma kan Daga Tutocin Rasha

Sunayen Jihohi da Bayanan 'Yan Siyasan Arewa da Ake Tuhuma kan Daga Tutocin Rasha

  • Rahotanni sun bayyana cewa jami'an tsaro sun fara bincikar wasu 'yan siyasa hudu daga Arewa kan zanga-zangar yunwa da ake gudanarwa
  • An ce ana tuhumar 'yan siyasar ne bisa zarginsu da hannu a daga tutocin kasar Rasha da masu zanga-zanga ke yi a wasu jihohin Arewa
  • Rahoto ya nuna cewa 'yan siyasar dai sun fito ne daga jihohin Katsina, Kaduna da Kano, kuma sun taka rawa mai girma a zaben 2023

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Jami'an tsaron Najeriya suna kan tuhumar akalla 'yan siyasa hudu daga shiyyar Arewa kan zargin daukar nauyin daga tutar kasar Rasha da masu zanga-zanga ke yi.

Kara karanta wannan

Masu zanga zanga sun ƙwace motar yaƙin ƴan sanda a Kaduna? Gaskiya ta fito

An ruwaito cewa jiga-jigan 'yan siyasar sun fito ne daga jihohin Katsina, Kaduna da kuma Kano.

Jami'an tsaro sun fara bincikar wasu 'yan siyasa kan daga tutocin rasha a lokacin zanga-zanga
Ana tuhumar wasu 'yan siyasa a Arewa yayin da masu zanga-zanga suka rika daga tutar Rasha. Hoto: @Miniko_jnr
Asali: Twitter

Tutar Rasha: Ana bincikar 'yan siyasar Arewa

Majiyoyi da dama sun shaidawa jaridar The Punch cewa ana zargin 'yan siyasar da hannu a ingiza masu zanga-zanga su daga tutar kasar wajen a Arewa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta saboda ba a bata hurumin yin magana kan lamarin ba ta ce:

"An gano manyan masu daukar nauyin daga tutar har mutum hudu. Sun kasance manyan 'yan siyasa ne daga Katsina, Kano da Kaduna kuma jami'an tsaro na bincikarsu.
"Wadannan jiga-jigan sun taka muhimmiyar rawa a babban zaben shekarar 2023 da ya gabata."

Ana zargin 'yan siyasan da karbo kwangila

Wata majiyar, wadda ita ma ta nemi a sakaya sunanta ta bayyana cewa:

"Akwai hujjoji da suka nuna cewa 'yan siyasar da aka bincika sun karbo kwangila daga wata kasa a Yammacin Afrika da Turai domin a daga tutar Rasha kamar yadda aka gani.

Kara karanta wannan

Legas: 'Yan daba sun kai mamaya kusa da ofishin gwamna, an tarwatsa masu zanga zanga

"Suna so ayi hakan a Najeriya kamar yadda aka yi a wasu kasashen."

A ranar Litinin ne aka ruwaito cewa zanga-zangar yunwa ta rikide zuwa wani abu na daban yayin da aka rika ganin wasu masu zanga-zanga daga Arewa suna daga tutar Rasha.

An daga tutar rasha a Kaduna

Legit Hausa ta ruwaito cewa masu zanga-zanga a Kaduna dauke da tutocin Rasha sun hau kan manyan titunan birnin jihar suna ihun "Ba mu yi," "Tinubu ya sauka," da sauransu.

Har ila yau, a jihar Kadunan ne aka ga masu zanga-zangar na satar kadarorin gwamnati da na gama garin mutane yayin da wasu suka yi dare-dare kan motar 'yan sanda.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.