Jerin Sanatoci da 'Yan Majalisun Tarayya 26 da Suka Rasu cikin Shekara 9 da Suka Gabata

Jerin Sanatoci da 'Yan Majalisun Tarayya 26 da Suka Rasu cikin Shekara 9 da Suka Gabata

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

FCT, Abuja - A cikin shekara tara da suka gabata (2015 zuwa 2024), Najeriya ta rasa ƴan majalisar dokoki ta tarayya da ke kan kujera aƙalla mutum 26.

Daga cikinsu akwai sanatoci takwas da ƴan majalisar wakilai mutum 18 waɗanda duk sun rasu ne a lokacin da jam'iyyar APC ke mulki a ƙasar nan.

Jerin 'yan majalisun da suka rasu daga 2015 zuwa 2024
Sanatoci da 'yan majalisar wakilai 29 suka rasu daga 2015 zuwa 2024 Hoto: Isa Dogonyaro, Hon Adams Abubakar Ekene, Sen. Dr. Patrick Ifeanyi Ubah
Asali: Facebook

Jaridar Leadership ta ce bincike ya nuna cewa ƴan majalisun waɗanda suka fito daga yankunan ƙasar nan, sun rasu ne sakamakon rashin lafiya yayin da guda ɗaya ya rasu saboda raunin harbin bindiga.

Sanatocin da suka rasu daga 2015 zuwa 2024

Sanatoci tara da ke kan kujera ne suka riga mu gidan gaskiya daga shekarar 2015 zuwa 2024. Ga jerinsu a nan ƙasa:

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Abin da Tinubu ya faɗawa hafsoshin tsaro kan masu ɗaga tutar Rasha

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Sanata Ahmed Zanna

Sanata Ahmed Zanna, wanda ke wakiltar Borno ta Tsakiya, ya rasu ne a shekarar 2015 yana da shekara 59, cewar rahoton jaridar Premium Times.

Kafin rasuwarsa ya yi fama da rashin lafiya wanda ya sanya ya samu ciwon sashi. Ya rasu bayan ya dawo daga Amurka inda ya je neman lafiya.

2. Sanata Isiaka Adetunji Adeleke

Sanata Isiaka Adetunji Adeleke ya yi sanata sau biyu kafin rasuwarsa. Ya wakilci Osun ta Yamma a majalisar dattawa a ƙarƙashin inuwar PDP a zaɓen 2007, an sake zaɓensa a zaɓen 2015 ƙarƙashin APC.

Sanatan ya rasu sakamakon ciwon zuciya a ranar 23 ga watan Afirilun 2017 a asibitin Biket da ke Osogbo a jihar Osun.

3. Sanata Ali Wakili

Sanata Ali Wakili wanda tsohon kwanturola na kwastam ne ya rasu lokacin da yake wakiltar Bauchi ta Yamma a majalisar dattawa a ranar, 17 ga watan Maris 2018.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: An kama mutumin da ke ɗinka tutocin ƙasar Rasha a jihar Kano

4. Sanata Benjamin Uwajumogu

Sanata Benjamin Uwajumogu ya rasu ne a ranar, 18 watan Disamban 2018 sakamakon rashin lafiya. Ya wakilci Imo ta Arewa a majalisar.

5. Sanata Ignatius Datong Longjan

Sanata Ignatius Datong Longjan ya je majalisa ne a shekarar 2019. Ya wakilci Plateau ta Kudu a majalisar kafin rasuwarsa a shekarar 2020.

Ya riƙe muƙamin mataimakin gwamnan jihar Plateau daga shekarar 2011 zuwa 2015.

6. Sanata Rose Okoji Oko

Sanata Rose Okoji Oko wacce ta wakilci Cross Rivers ta Arewa ta rasu ne a ranar 23 ga watan Maris 2020.

7. Sanata Adebayo Sikiru Osinowo

Sanata Adebayo Sikiru Osinowo wanda ya wakilci Legas ta Gabas ya rasu ne a ranar, 15 ga watan Yunin 2020.

8. Sanata Patrick Ifeanyi Ubah

Sanata Patrick Ifeanyi Ubah wanda sanannen ɗan kasuwa ne ya rasu ne a birnin Landan a ranar, 27 ga watan Yulin 2024.

Ƴan majalisar wakilai da suka rasu daga 2015 zuwa 2024

Kara karanta wannan

Wani bom ya tarwatse a teburin mai shayi, mutane kusan 20 sun mutu a Arewa

9. Honarabul Olatoye Temitope Sugar 

Honarabul Olatoye Temitope da ke wakiltar Lagelu/Akinyele ya rasu ne a ranar, 9 ga watan Maris 2019.

An harbe shi ne a ƙauyen Lalupon da ke ƙaramar hukumar Lagelu da ke jihar Ibadan. An garzaya da shi asibiti a Ibadan inda ya rasu a can.

10. Honarabul Ja'afaru Iliyasu

Ja'afaru Iliyasu wanda ya wakilci mazaɓar Magama/Rijau a majalisar wakilai daga jihar Neja ya rasu ne a watan Satumban 2019.

11. Hon Mohammed Adamu Fagen Gawo

Honarabul Mohammed Adamu Fagen Gawo ya rasu ne yayin da ke wakiltar mazaɓar Garki/Bubara daga jihar Jigawa.

Ya rasu ne a shekarar 2019 a Dubai bayan yaje neman lafiya.

12. Honarabul Bello Sani

Bello Sani wanda ya wakilci Mashi/Dutsi daga jihar Katsina ya rasu yana da shekara 51 a ranar, 15 ga watan Fabrairun 2017.

13. Honarabul Umar Buba Jibril

Umar Buba Jibril wanda ya wakilci Lokoja/Kogi/Koton Karfe daga jihar Kogo ya rasu yana da shekara 57 a wani asibiti a birnin tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Ana saura kwana 1, gwamnatin Tinubu ta aike da muhimmin saƙo kan zanga zanga

14. Honarabul Elijah Adewale

Elijah Adewale kafin rasuwarsa shi ne ɗan majalisa mai wakiltar Ifako Ajaiye daga jihar Legas.

Ya faɗi ya rasu ne da safiyar ranar, 21 ga watan Yulin 2016 a gidansa da ke Abuja.

15. Honarabul Musa Baba-Onwama

Honarabul Musa Baba-Onwama ya wakilci Nasarawa/Toto daga jihar Nasarawa. Ya rasu yana da shekara 50 a duniya.

Sauran su ne:

16. Honarabul Abdullahi Wamakko

17. Honarabul Yuguda Hassan Kila

18. Prestige Ossy

19. Adebayo Omolafe

20. Haruna Maitala

21. Sulaiman Lere

22. Ekpenyong Bassey

23. Abdulkadir Danbuga

24. Isa Dogonyaro

25. Musiliudeen Akinremi

26. Abubakar Adams Ekene

Tinubu ya dawo da tallafin man fetur

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa an dawo da tallafin fetur da Shugaba Bola Tinubu ya cire a shekarar 2023.

Olusegun Obasanjo ya ce Shugaba Tinubu ya dawo da biyan tallafin fetur din ne sakamakon hauhawar farashin kayayyaki da kasar ke fuskanta.

Kara karanta wannan

'Yan ta'addan Boko Haram sun sake dasa bam, ya hallaka babban jami'in gwammnati a Borno

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng