Rana ta 5: Duk da Barazanar 'Yan Daba, Masu Zanga Zanga Sun Sake Fitowa

Rana ta 5: Duk da Barazanar 'Yan Daba, Masu Zanga Zanga Sun Sake Fitowa

  • Masu gudanar da zanga-zanga a jihar Legas sun nuna jarumta bayan sake fitowa filin Ojota bayan 'yan daba sun fatattakesu
  • 'Yan daba sun kori masu gudanar da zanga-zangar adawa da manufofin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu a ranar Lahadi
  • Wasu masu zanga-zangar sun bayyana cewa ba za su daina fitowa ba har sai Tinubu da dauki makan share masu hawaye

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Legas - Wasu 'yan Najeriya sun sake fitowa filin Freedom Park da ke Ojota a jihar Legas duk da tarwatsa taronsu da 'yan daba su ka yi ranar Lahadi.

Wasu daga cikin jagororin kungiyoyin da ke gudanar da zanga-zanga sun bayyana janyewarsu bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi jawabin neman tattaunawa.

Kara karanta wannan

Masu zanga zanga na daga tutar Rasha a Kaduna, an fara awon gaba da kayan jama'a

Benson Ibeabuchi
An sake fitowa zanga zanga a ranar ta 5 a Legas Hoto: Benson Ibeabuchi
Asali: Getty Images

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa amma wasu kungiyoyin matasa, na Socialist Workers League da Democratic Social Movement sun ce za su ci gaba da neman hakkinsu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Za mu cigaba da fitowa zanga-zanga," Matasa

Matasa a jihar Legas sun fito ci gaba da zanga-zangar lumana a jihar duk da lamarin ya rikide zuwa rikici a wasu jihohin, wasu kuma 'yan daba su ka koresu.

Jaridar Premium Times ta wallafa cewa an samu 'yar hatsaniya tsakanin masu zanga-zanga da jami'an tsaron da su ka dauke motar daya daga cikinsu.

Wata Precious Oruche da ta fito zanga-zangar ta ce za su ci gaba da neman hakkinsu, domin ko kadan shugaban kasa bai duba matsalolin kasar nan ba.

An kafa kwamitin kan kisan masu zanga-zanga

A baya mun ruwaito cewa gwamnatin jihar Kano ta samar da kwamitin da zai yi bincike a kan kisan mutane da dama da suka fito zanga-zanga a wasu daga cikin unguwannin Kano.

Kara karanta wannan

Matsin rayuwa: Bayan rasa rayuka, masu zanga zanga sun fara alkunutu a Kano

Daga cikin wasu ayyukan da kwamitin zai yi akwai binciken wasu da ake zargin 'yan daban haya ne su ka rika kwace kayan jama'a da sace wadansu a sassa daban-daban na jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.