“Babu Mai Hana Ni Darewa Sarauta”: Tsohon Gwamna Ya Sha Alwashi Kan Karaga

“Babu Mai Hana Ni Darewa Sarauta”: Tsohon Gwamna Ya Sha Alwashi Kan Karaga

  • Yayin da aka naɗa sabon Olubadan na Ibadan, tsohon gwamnan Oyo ya sha alwashin darewa sarautar a nan gaba
  • Rashidi Ladoja ya ce babu mai hana shi samun sarautar idan har ubangiji ya ƙaddara masa haka a rayuwarsa
  • Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin Oyo da ta shude da Gwamna Seyi Makinde sun kawo sauye-sauye a tsarin sarautar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo - Tsohon gwamnan jihar Oyo, Rashidi Ladoja ya yi magana kan neman sarautar Olubadan mai daraja a jihar.

Ladoja ya ce idan yana raye babu wanda zai hana shi darewa sarautar Olubadan komai daren dadewa a jihar.

Tsohon gwamnan ya bayyana kwadayinsa kan kujerar sarauta
Tsohon gwamnan Ooyo, Rashidi Ladoja ya sha alwashin zama Olubadan na Ibadan. Hoto: Rashidi Adewolu Ladoja.
Source: Facebook

Oyo: Ladoja ya sha alwashin zama Olubadan

Kara karanta wannan

Bayan gwamna a Arewa ya ki albashin N70,000, NLC ta fadi matakin da za ta dauka

Tsohon gwamnan ya bayyana haka a jiya Lahadi 4 ga watan Agustan 2024 a cikin wata sanarwa, cewar the Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ladoja ya amince da karbar sandan sarauta ta musamman a matsayin wani mataki na zama Olubadan a gaba.

"Zan karbi sandar sarautar idan wannan shi ne ya hana ni zama Olubadan na kasar ibadan."

- Rashidi Ladoja

Yadda gwamnatoci suka sauya tsarin sarautar Olubadan

Ladoja ya sha takun-saka da tsohon gwamnan jihar, Abiola Ajimobi wanda ya yi kokarin kawo sauyi a tsarin sarautar, cewar Punch.

Rahotanni sun tabbatar da cewa Ladoja shi ne a kan layi wanda zai gaji sarautar Olubadan duk da sauya tsare-tsaren da Gwamna Seyi Makinde ya yi a yanzu.

Matakin Gwamna Makinde ya kawo rudani a jihar inda ake ganin yana da wata manufa.

Tsohon gwamnan ya ce babu mai iya hana shi zama Olubadan na gaba idan har Allah ya ƙaddara masa hakan.

Zanga-zanga: Gaskiya kan hari a gidan Buhari

Kara karanta wannan

"Jami'an tsaro sun gano sanata mai daukar nauyin zanga zanga," Minista Wike ya yi magana

Kun ji cewa Masarautar Daura ta yi magana bayan jita-jitar cewa masu zanga-zanga sun dira gidan sarkin da na Muuhammadu Buhari.

An ruwaito cewa wasu masu zanga-zanga sun yi dafifi a gidan tsohon shugaban kasa da kuma Sarkin Daura a jihar Katsina.

Kakakin Sarkin Daura, Usman Ibrahim Yaro ya musanta cewa matasan sun taba gidajen Buhari da na sarkin inda ya ce wucewa suka yi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.