“Babu Mai Hana Ni Darewa Sarauta”: Tsohon Gwamna Ya Sha Alwashi Kan Karaga

“Babu Mai Hana Ni Darewa Sarauta”: Tsohon Gwamna Ya Sha Alwashi Kan Karaga

  • Yayin da aka naɗa sabon Olubadan na Ibadan, tsohon gwamnan Oyo ya sha alwashin darewa sarautar a nan gaba
  • Rashidi Ladoja ya ce babu mai hana shi samun sarautar idan har ubangiji ya ƙaddara masa haka a rayuwarsa
  • Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin Oyo da ta shude da Gwamna Seyi Makinde sun kawo sauye-sauye a tsarin sarautar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo - Tsohon gwamnan jihar Oyo, Rashidi Ladoja ya yi magana kan neman sarautar Olubadan mai daraja a jihar.

Ladoja ya ce idan yana raye babu wanda zai hana shi darewa sarautar Olubadan komai daren dadewa a jihar.

Tsohon gwamnan ya bayyana kwadayinsa kan kujerar sarauta
Tsohon gwamnan Ooyo, Rashidi Ladoja ya sha alwashin zama Olubadan na Ibadan. Hoto: Rashidi Adewolu Ladoja.
Asali: Facebook

Oyo: Ladoja ya sha alwashin zama Olubadan

Kara karanta wannan

Bayan gwamna a Arewa ya ki albashin N70,000, NLC ta fadi matakin da za ta dauka

Tsohon gwamnan ya bayyana haka a jiya Lahadi 4 ga watan Agustan 2024 a cikin wata sanarwa, cewar the Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ladoja ya amince da karbar sandan sarauta ta musamman a matsayin wani mataki na zama Olubadan a gaba.

"Zan karbi sandar sarautar idan wannan shi ne ya hana ni zama Olubadan na kasar ibadan."

- Rashidi Ladoja

Yadda gwamnatoci suka sauya tsarin sarautar Olubadan

Ladoja ya sha takun-saka da tsohon gwamnan jihar, Abiola Ajimobi wanda ya yi kokarin kawo sauyi a tsarin sarautar, cewar Punch.

Rahotanni sun tabbatar da cewa Ladoja shi ne a kan layi wanda zai gaji sarautar Olubadan duk da sauya tsare-tsaren da Gwamna Seyi Makinde ya yi a yanzu.

Matakin Gwamna Makinde ya kawo rudani a jihar inda ake ganin yana da wata manufa.

Tsohon gwamnan ya ce babu mai iya hana shi zama Olubadan na gaba idan har Allah ya ƙaddara masa hakan.

Kara karanta wannan

"Jami'an tsaro sun gano sanata mai daukar nauyin zanga zanga," Minista Wike ya yi magana

Zanga-zanga: Gaskiya kan hari a gidan Buhari

Kun ji cewa Masarautar Daura ta yi magana bayan jita-jitar cewa masu zanga-zanga sun dira gidan sarkin da na Muuhammadu Buhari.

An ruwaito cewa wasu masu zanga-zanga sun yi dafifi a gidan tsohon shugaban kasa da kuma Sarkin Daura a jihar Katsina.

Kakakin Sarkin Daura, Usman Ibrahim Yaro ya musanta cewa matasan sun taba gidajen Buhari da na sarkin inda ya ce wucewa suka yi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.