Gwamnatin Kaduna ta Sanya Dokar Hana Fita? Uba Sani ya Magantu Ana Zanga Zanga

Gwamnatin Kaduna ta Sanya Dokar Hana Fita? Uba Sani ya Magantu Ana Zanga Zanga

  • Gwamnan Kaduna, Uba Sani ya karyata rahoton da ke yawo cewa ya kakaba dokar hana fita ta awanni 24 a jihar saboda zanga zanga
  • Rahotanni sun bayyana cewa masu zanga zanga sun lalata kadarorin gwamnnati da kuma sace dukiyoyin gwamnati da na jama'a
  • Sai dai a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, gwamnan ya ce komai ya dawo dai dai a yanzu, kuma ba a sanya wata doka ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kaduna - Wani rahoto da ya karade shafukan sada zumunta ya nuna gwamnatin Kaduna ta sanya dokar hana fita ta awanni 24 sakamakon zanga-zanga.

An ce gwamnatin ta sanya dokar ne biyo bayan kona kadarorin gwamnati da satar dukiyar jama'a da 'yan daba suka rika yi ana tsaka da yin gangamin.

Kara karanta wannan

Wani gwamnan Arewa ya sake hana zanga zanga, an sanya dokar awa 24 babu fita

Gwamna Uba Sani ya yi magana kan sanya dokar ta baci a Kaduna
Gwamnatin Kaduna ta ce ba a sanya dokar ta baci ba tukunna. Hoto: @ubasanius
Asali: Twitter

An sanya dokar ta-baci a Kaduna?

Sai dai Gwamna Uba Sani ya karyata wannan rahoto, inda ya wallafa a shafin gwamnan jihar a Facebook, ya ce gwamnatin Kaduna ba ta sanya dokar ta baci ba tukunna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A ranar Alhamis, Gwamna Uba Sani ya ce tuni gwamnati da jami'an tsaro a jihar suka shawo kan tashin hankalin da ke faruwa a sassan jihar

Jaridar Leadership ta ruwaito gwamnan ya rubuta cewa:

“A yanzu haka da nake magana, ba a sanya dokar hana fita ba a Kaduna. Komai ya dawo dai dai a yanzu."

Kaduna: An kona ofishin KATSLEA

Legit Hausa ta ruwaito cewa wasu 'yan daba da suka saje da masu zanga-zanga sun kai farmaki ofishin hukumar KASTLEA inda suka cinnawa ginin wuta.

An ce bayan kona wani bangare na ginin, 'yan daban sun kuma wawushe wasu kayayyaki da aka ajiye a ciki, inda daga bisani suka fasa gidaje da shagunan jama'a.

Kara karanta wannan

Jihohin Arewa da aka sanya dokar hana fita ta awa 24 sun kai 4, an samu cikakken bayani

A hannu daya kuma, jami'an 'yan sandan sun fara harbi kan masu zanga-zanga a wasu sassa na jihar Kaduna domin kwantar da tarzoma.

Kalli bidiyon a kasa:

An sanya dokar ta baci a jihohi

A wani labarin, mun ruwaito cewa zuwa yanzu jihohin Arewa uku ne aka sanya dokar hana fita ta awanni 24 bayan fashewar bam da kuma munanar zanga-zanga.

Yayin da Kano da Yobe suka sanya dokar hana fita saboda tashin hankula da aka samu sanadin zanga-zanga, gwamnatin Borno ta sanya dokar ne bayan fashewar bam.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.