Zanga Zanga: Matasa Sun Fandare, Sun Nufi Gidajen Manyan Najeriya a Abuja

Zanga Zanga: Matasa Sun Fandare, Sun Nufi Gidajen Manyan Najeriya a Abuja

  • Matasa da ke zanga-zanga a Abuja sun sauya salo inda suka durfafi yankin Asokoro da ke birnin duk da barazanar jami'an tsaro
  • Mazu zanga-zangar sun yi yunkurin shiga Asokoro duk da barazana daga jami'an tsaro da kuma harbe-harbe
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake cigaba da gudanar da zanga-zanga a fadin kasar saboda tsadar rayuwa a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Masu zanga-zanga a birnin Abuja sun durfafi yankin Asokoro inda ke dauke da manyan kasar Najeriya.

Matasan suna kokarin kutsa kai ne duk da harbe-harben jami'an tsaro yayin da ake cigaba da zanga-zanga.

Manya sun shiga matsala yayin da masu zanga-zanga suka tinkari Asokoro
Masu zanga-zanga sun nemi kutsawa cikin Asokoro da ke birnin Abuja. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Zanga-zanga: Matasa sun farmaki Asokoro a Abuja

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Gwamna Abba ya sanya dokar hana fita a Kano, ya umarci jami'an tsaro

Daily Trust ta tabbatar da cewa Asokoro ne inda mafi yawan manyan Najeriya da ke mulki ke rayuwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sannan a wurin akwai manyan gine-ginen gwamnati da barikokin sojoji da kuma ofishin DSS.

A cikin wani faifan bidiyon an gano yadda matasan suke cigaba da kutsawa duk da harbin barkwanon tsohuwa domin dakile su.

Zanga-zanga ta rikide a jihohin Arewacin Najeriya

Wannan na zuwa ne yayin da ake cigaba da zanga-zanga a fadin kasar da ya rikide ya koma tashin hankali.

A jihohi da dama masu zanga-zangar sun ci karo da matsala yayin da miyagu suka shiga ciki domin biyan bukatar kansu.

Jihohin Kano da Borno da Yobe tuni suka sanya dokar hana fita domin dakile cigaba da barnar da ake yi a zanga-zangar.

'Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga

Kun ji cewa jami’an ‘yan sandan kasar nan sun tarwatsa daruruwan masu zanga-zanga da borkonon tsohuwa a filin Eagle da ke babban birnin tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Kaduna: Masu zanga zanga sun kona ofishin KASTLEA, sun wawashe dukiyar jama'a

‘Yan sandan sun bayyana cewa sun dauki matakin ne domin tabbatar da umarnin kotu na cewa masu zanga-zanga su tsaya a filin wasa na Moshood Abiola.

Rahotanni sun tabbatar cewa da yawa daga cikin masu zanga-zangar sun nemi mafaka a sassa daban-daban yayain da wasu su ka nuna ko in kula.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.