Kotu Ta Yi Hukunci Kan Masu Shirin Zanga Zanga, Ta Gindaya Sharuda Masu Tsauri

Kotu Ta Yi Hukunci Kan Masu Shirin Zanga Zanga, Ta Gindaya Sharuda Masu Tsauri

  • Ana shirin fita zanga-zanga a jihar Ogun, Babbar Kotun jihar ta yi hukunci, inda ta ba matasa umarni kan lamarin
  • Kotun ta umarci masu gudanar da zanga-zangar da su yi a wurare guda hudu kacal a jihar bayan shigar da korafi gabanta
  • Legit Hausa ta ji ta bakin wani shugaban kungiyar matasa kan wannan hukunci na kotu a jihar Ogun kan zanga-zangar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ogun - Babbar Kotun jihar Ogun ta yi zama kan masu zanga-zanga a jihar inda ta ba su umarni yadda za su gudanar da ita.

Kotun ta umarce su da su gudanar da zanga-zangar a wurare hudu kacal a fadin jihar sabanin yadda suka shirya.

Kara karanta wannan

Zanga zanga ta barke a Kano ana daf da fita ta gama gari, bayanai sun fito

Kotu ta gindaya sharuda ga masu zanga-zanga a Ogun
Kotu a jihar Ogun ta umarci gudanar da zanga-zanga a wurare hudu kacal. Hoto: @DapoAbiodunCON.
Asali: Twitter

Zanga-zanga: Kotu ta gidanya sharuda ga matasa

Punch ta tabbatar da cewa kotun ta rage lokacin gudanar da zanga-zangar daga 8.00 na safe zuwa karfe 5.0O na yamma a jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Alkalin kotun. Mai Shari'a, O. Ogunfowora shi ya dauki wannan mataki a yau Laraba 31 ga watan Yulin 2024, cewar TheNigeriaLawyer.

Ogunfowora ya umarce su da yin zanga-zangar a filin wasa na MKO Abiola da makarantar Ansar-ud-Deen da ke Ota.

Sauran wuraren sun hada da babbar makarantar Remo da ke Sagamu da kuma filin wasa na Dipo Dina da ke Ijebu-Ode.

Wannan na zuwa ne bayan korafin da kwamishinan shari'a a jihar, Oluwasina Ogungbade ya shigar a gaban kotun.

Tattaunawar Legit Hausa da wani matashi

Legit Hausa ta ji ta bakin wani shugaban kungiyar matasa kan wannan hukunci na kotu a Ogun.

Kara karanta wannan

"Ka samar mana da motoci": Masu zanga zanga sun tura bukatunsu ga gwamna

Kwamred Kabir Haruna ya ce kwata-kwata hakan bai dace ba saboda dakile shirin kwatar ƴanci ne.

"Wannan wata hanya ce ta kashe karfin guiwar matasa idan aka ce sai wasu zababbun wurare za a yi zanga-zanga."
"Musabbabin gudanar da zanga-zangr shi ne gwamnatin ta san da halin da jama'a ke ciki."

- Kabir Haruna

Matasa sun fito zanga-zanga a Kano

Kun ji cewa daruruwan mutane a jihar Kano sun fito kan tituna inda suke adawa da zanga-zangar da za a yi a gobe.

Mutanen sun cika titunan birnin ne a yau Laraba 31 ga watan Agustan 2024 domin nuna rashin goyon baya ga zanga-zanga.

Kungiyar da ke goyon bayan Shugaba Bola Tinubu ta tabbatar da cewa shugaban yana kokarin kawo sauki a kasar baki daya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.