Ohanaeze: Dalilin da Ya Sa Matasan Ibo Ba Za Su Shiga Zanga Zangar Yunwa Ba

Ohanaeze: Dalilin da Ya Sa Matasan Ibo Ba Za Su Shiga Zanga Zangar Yunwa Ba

  • Matasan Ibo sun yanke shawarar ficewa daga cikin shirin zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a farkon watan Agusta
  • Kungiyar Ibo ta Ohanaeze Ndigbo ce ta sanar da hakan bayan ganawa da matasan kan matsalolin shiyyar Kudu maso Gabas
  • Shugaban matasan Hausawa mazauna Enugu, Aliyu Adamu Kwankwaso ya shaidawa Legit Hausa matsayarsu kan zanga-zangar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Enugu - Kungiyar raya kabilar Ibo, Ohanaeze Ndigbo ta ce matasan Ibo ba za su shiga zanga-zangar yunwa da ake shirin yi daga 1 zuwa 10 ga Agusta ba.

Kungiyar Ohanaeze ta yi magana ne da 'yan jarida a Enugu a ranar Litinin bayan taron gaggawa na kungiyar matasan Ibo mai taken "Halin da kasa ke ciki."

Kara karanta wannan

Rana Ta 2: Rundunar Sojoji ta shirya ɗaukar mataki mai tsauri kan masu zanga zanga

Ohanaeze ta yi magana kan shigar matasan Ibo zanga-zangar yunwa
Ohanaeze ta ce matasan Ibo ba za su shiga zanga-zangar yunwa ba. Hoto: @Ohanaezendigboo
Asali: Twitter

Jaridar The Punch ta ruwaito Ohanaeze ta ce tabbas shiyyar Kudu maso Gabas na da dalilan shiga wannan zanga-zangar, amma ba za su shiga ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ohanaeze ta magantu kan zanga-zanga

Dalilan shiga zanga-zangar da kungiyar ta zayyana sun hada da matsin tattali, rashin aikin yi, rashin shugabanci mai kyau a shiyyar.

Da yake karanta matsayar kungiyar, shugaban Ohanaeze, Chukwuma Okpalaezeukwu, ya ce matasan Ibo za su kauracewa zanga-zangar kamar yadda iyayensu suka yi.

Chukwuma Okpalaezeukwu ya ce maimakon wannan zanga-zangar, matasan za su zauna da gwamnati domin tattaunawa tare da shawo kan matsalolin da suka ambata.

Dalilin Ibo na kauracewa zanga-zanga

Bayan tattaunawa da matasan yankin, kungiyar ta yanke shawarar tattaunawa da gwamnatin tarayya da gwamnonin Kudu maso Gabas domin nemo hanyoyin magance matsalolin shiyyar.

Wannan matakin, a cewar kungiyar, zai kara karfafa alakar gwamnati da kungiyar maimakon yin fito na fito da gwamnati da ka iya haddasa rikici, inji rahoton New Telegraph.

Kara karanta wannan

Kano: 'Yan sanda sun saki bidiyon masu zanga zanga suna wawushe dukiyar jama'a

Shugaban Ohanaeze wanda ya jaddada cewa zanga-zanga 'yanci ne na dan kasa, sai dai ya nuna fargaba cewa hakan na iya kai ga rasa rayuka, asarar dukiya kamar dai lokacin zanga-zangar EndSARS a 2022.

Matasan Hausawan Enugu sun magantu

A zantawarmu da Aliyu Adamu Kwankwaso, shugaban kungiyar matasan Hausawan jihar Enugu, ya ce su ma ba za su shiga wannan zanga-zangar ba.

A cewar Aliyu Kwankwaso, kungiyar ta fi son tattaunawa da gwamnati cikin lumana ba tare da hayaniya ba maimakon fitowa zanga-zangar nuna adawa.

Hausawan da ke zama a Enugu sun bukaci gwamnatin jihar da ma ta tarayya da su baiwa matasa damar zama a teburin sasanci domin nemo hanyoyin cigaban matasa baki daya.

'Yan sanda sun sanya dokar ta baci?

A wani labarin, mun ruwaito cewa rundunar 'yan sanda ta ce sufeta janar (IGP) Kayode Egbetokun bai bayar da umarni na sanya dokar ta baci lokacin zanga-zanga ba.

Kara karanta wannan

Ana fargabar miyagu za su shiga zanga zanga, an samu hanyoyi 5 domin kare kai

Rundunar ta ce rahoton da aka ce za a sanyawa masu zanga-zanga dokar tashi karfe 4 na yamma ba gaskiya bane, kirkirarren labari ne da aka yada domin cimma wata manufa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.