Rai Bakon Duniya: Tsohon Kwamishina a Kaduna Ya Kwanta Dama

Rai Bakon Duniya: Tsohon Kwamishina a Kaduna Ya Kwanta Dama

  • An shiga jimami a jihar Kaduna bayan rasuwar tsohon kwamishina kuma fitaccen dan jarida a jiya Asabar 27 ga watan Yulin 2024
  • Marigayin mai suna Alhaji Lawal Yusufu Saulawa ya rasu yana da shekaru 80 a duniya inda aka yi jana'izarsa a yau Lahadi a Kaduna
  • Kafin rasuwar marigayin ya rike kwamishinan yada labarai a jihar Kaduna shekaru 40 da suka wuce da kuma aiki da BBC Hausa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - Fitaccen dan jarida a Najeriya, Alhaji Lawal Yusufu Saulawa ya riga mu gidan gaskiya a jihar Kaduna.

Marigayin wanda tsohon kwamishina ne a jihar ya rasu a daren jiya Asabar 27 ga watan Yulin 2024 yana da shekaru 80.

Kara karanta wannan

Sunayen Sanatoci da ‘Yan majalisar tarayya 6 da mutuwa ta dauke bayan cin zaben 2023

Tsohon kwamishina kuma dan jarida ya kwanta dama
Tsohon kwamishina kuma ma'aikacin BBC Hausa, Lawal Saulawa ya rasu. Hoto: BBC Hausa.
Asali: Facebook

Yaushe Saulawa ya rasu a Kaduna?

BBC Hausa ta tattaro cewa marigayin ya rasu a gidansa da ke Badikko a karamar hukumar Kaduna ta Kudu inda aka binne shi a makabartar Bashama.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gudanar da sallar jana'izarsar masallacin Juma'a na Danfodio da ranar yau Lahadi 28 ga watan Yulin 2024.

Sallar jana'zarsa ta samu halartar manya mutane wadanda suka nuna alhini game da rasuwar marigayin.

Kaduna: Mukaman da Saulawa ya rike

Saulawa ya yi aiki da gidan jaridar BBC Hausa shekaru fiye da 40 da suka wuce kafin ya rike kwamishinan yada labarai a Kaduna.

Har ila yau, marigayin shi ne kwamishinan farko na yada labarai a jihar Katsina da sauran mukamai da dama.

Marigayin ya rasu ya bar mata uku da 'ya'ya guda 13 da kuma tulin jikoki da sauran 'yan uwa a bayansa.

Kara karanta wannan

An shiga jimami bayan Sanatan APC mai ci ya riga mu gidan gaskiya

Sanatan APC, Ubah ya rasu a Landan

A wani labarin, mun kawo muku labarin cewa an tafka babban rashin sanatan APC, Sanata Ifeanyi Ubah daga jihar Anambra.

Marigayin da ya wakilci Anambra ta Kudu ya rasu ne a birnin Landan da ke Burtaniya bayan ya sha fama da jinya na kankanin lokaci.

Majalisar Dattawa ta tabbatar mutuwar Ubah a jiya Asabar 27 ga watan Yulin 2024 inda ta ce an tafka babban rashin mutum nagari.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.