Rundunar 'yan Sanda ta Gano Manyan Matsalolin da Zanga Zanga Za Ta Iya Haifarwa

Rundunar 'yan Sanda ta Gano Manyan Matsalolin da Zanga Zanga Za Ta Iya Haifarwa

  • Hadakar hukumomin tsaro sun kammala daukar matakai a kan masu niyyar fita zanga-zanga ranar 1 Agusta, 2024
  • A wata hira da ta kebanta da Legit, rundunar 'yan sandan Jigawa ta bayyana cewa ta zauna da masu ruwa da tsaki a kokarin shawo kan jama'a
  • Jami'an hulda da jama'a na rundunar, DSP Lawan Shiisu Adam ya ce sun gudanar da gagarumin taro domin dakile zanga zangar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Jigawa - Yayin da ya rage kwanaki uku a fara zanga-zangar gama gari a kasar nan, rundunar 'yan sandan jihar Jigawa ta fitar da tsare-tsaren tunkarar lamarin.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun ba matasa damar zanga zanga, sun gindaya musu sharuda masu tsauri

Jami'in hulda da jama'a na rundunar, DSP Lawan Shiisu Adam ya bayyana cewa sun yi kokarin nusar da jama'a illar gudanar da zanga-zanga.

Jigawa map
Rundunar 'yan sanda na tsoron zanga-zanga zai haifar da rikici Hoto: Legit.ng
Asali: Original

DSP Lawan Shiisu Adam ya shaidawa Legit cewa sun zauna da masu ruwa da tsaki, daga ciki har da sarakuna, malaman addini, hukumomi, kungiyoyi masu zaman kansu da mata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Fargabar 'yan sanda a kan zanga-zanga

Rundunar 'yan sanda ta bayyana tsoron tsunduma tashe-tashen hankula da wargajewar al'umma a lokacin zanga-zanga.

DSP Lawan Shiisu Adam da ke magana da yawun rundunar reshen jihar Jigawa ne ya bayyana haka, inda ya bayyana wasu daga matsalolin da za a iya samu;

1. Miyagu za su shiga zanga-zanga

DSP Adam ya ce akwai fargabar wadanda za su tayar da tarzoma tuni su ka kammala shirin jawo tashe-tashen hankula ta rigar masu zanga-zanga.

Ya ce akwai wasu kasashen ketare da za a iya ganin yadda miyagu su ka shiga cikin masu zanga-zanga. kuma har yanzu ana fama da matsalolin tsaro.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Rundunar 'yan sanda ta dauki mataki a Abuja, ta fadi shirinta

2. Lalata dukiyoyin jama'a a lokacin zanga-zanga

Kakakin rundunar 'yan sandan Jigawa ya shaida cewa akwai fargabar wasu bata gari ka iya amfani da rigar zanga-zanga wurin lalata kayan jama'a.

DSP Lawan Shiisu Adam ya kara da cewa idan aka samu irin wannan akasi, za a iya lalata kadarorin gwamnati, dukiyoyin jama'a, rumbunan abinci da satar kayan 'yan kasuwa.

3. Asarar rayukan idan miyagu sun shiga zanga-zanga

'Yan sanda Jigawa sun bayyana cewa akwai fargabar idan zanga-zanga ta sauya launi daga kalar lumana zuwa tashin hankali za a samu asarar rayuka.

Kakakin rundunar, DSP Lawan Shiisu Adam ya ce barin zanga-zanga da hawa teburin tattaunawa shi zai fi alheri.

Zanga-zanga: Yan sanda za su bayar da tsaro

A wani labarin kun ji cewa rundunar 'yan sandan kasar nan ta bayyana shirinta na dakile tashe-tashen hankula yayin zanga-zangar kwanaki 10 da 'yan kasa ke shirin yi.

Rundunar reshen babban birnin tarayya Abuja ta ce za ta tura jami'anta 4,200 zuwa lungu da sakon birnin a kokarinta na kare rayuka da dukiyoyin jama'a yayin zanga-zanga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.